Nijeriya

Aƙalla mutum 10 sun mutu, bakwai sun jikkata bayan fashewar bam a Jihar Zamfaran Nijeriya

Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 6:15 na yammacin ranar Litinin, lokacin da wata motar Volkswagen Golf da ke ɗauke da fasinjoji daga Bagega zuwa Anka a Ƙaramar Hukumar Anka ta taka bam ɗin da aka dasa a kan hanya.

Newstimehub

Newstimehub

11 Jun, 2026

21528263 25efa39c 1ca0 4433 be7f 63aa63c4c16e 720 main

Aƙalla mutum 10 sun rasa rayukansu yayin da wasu bakwai suka jikkata bayan wata motar haya ta taka wani bam ƙirar gida (IED) da ake zargin ’yanta’adda ne suka dasa a kan hanyar Bagega zuwa Anka a Jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Nijeriya, a cewar majiyoyin tsaro.

Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 6:15 na yammacin ranar Litinin, lokacin da wata motar Volkswagen Golf da ke ɗauke da fasinjoji daga Bagega zuwa Anka a Ƙaramar Hukumar Anka ta taka bam ɗin da aka dasa a kan hanya.

Fashewar ta lalata motar gaba ɗaya tare da jawo asarar rayuka da raunuka masu yawa, yayin da aka garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa cibiyoyin lafiya domin samun kulawa.

Kakakin rundunar ’yansandan Jihar Zamfara, Yazid Abubakar, ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Anadolu cewa an tura wata haɗaɗɗiyar tawagar tsaro da ta ƙunshi jami’an Sashen Yaki da Manyan Laifuka na rundunar ’yansandan jihar da kuma masu aikin tsaron sa-kai, ƙarƙashin jagorancin kwamishinan ’yansanda, domin tabbatar da tsaro a kan hanyar da kuma hana sake kai irin wannan hari.

Ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike kan wannan fashewa.

Rahotanni sun nuna cewa ’yanta’addan da ake kira ’yanbindiga a yankin ne suka dasa bam ɗin.

Waɗannan ƙungiyoyi sun daɗe suna addabar Zamfara da wasu jihohin makwabta ta hanyar satar mutane domin neman kuɗin fansa, kashe-kashe da kai hare-hare kan al’ummomin karkara.

Wannan hari ya ƙara tayar da hankali kan yadda ƙungiyoyin masu aikata laifuka ke ƙara amfani da abubuwan fashewa a arewa maso yammacin Nijeriya, yankin da ke fama da matsanancin matsalar tsaro duk da ci gaba da ayyukan soji.

Hanyar Bagega zuwa Anka ta sha fama da irin waɗannan hare-hare a cikin watannin baya-bayan nan.

A watan Mayu ma, aƙalla mutum shida sun mutu yayin da wasu da dama suka jikkata bayan wata motar haya ta taka wani bam makamancin wannan a kan wannan hanya.

Bayan harin na watan Mayu, jami’an tsaro sun gudanar da aikin bincike da share hanyar tare da takaita zirga-zirga na ɗan lokaci.

Jihar Zamfara na daga cikin jihohin Nijeriya da suka fi fama da matsalar hare-haren ’yanbindiga.

Ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai da ke fakewa a dazukan yankin na ci gaba da kai hare-hare kan hanyoyi, ƙauyuka da matafiya, lamarin da ke ƙara nuna damuwa game da sabbin dabarun da suke amfani da su da kuma yaɗuwar amfani da bama-bamai zuwa arewa maso yammacin ƙasar, inda a baya irin waɗannan makamai suka fi shahara a arewa maso gabas.