Nijeriya

Sojojin Nijeriya sun kashe ’yanta’adda 662, sun ceto 951 da aka sace cikin watanni uku

Hedkwatar Tsaron Nijeriyar ta ce dakarunta sun kashe ’yanta’adda 662 da sauran gungun masu laifi, sun kama mutane 1,084 da ake zargi, kuma sun ceto mutane 951 da aka yi garkuwa da su a faɗin ƙasar a  zango na biyu na shekarar 2026.

Newstimehub

Newstimehub

2 Jul, 2026

a9466900cad616afbbdda2d9b8f2cdbd15fef13bd5adb0467be32a999ac3a931

Hedkwatar Tsaron Nijeriya ta bayyana cewa samamen da aka ƙaddamar bisa dogaro da bayanan sirri ya yi sanadiyyar kashe ’yanta’adda 662 da kama mutane 1,084 da ake zargi, da kuma ceto mutane 951 da aka sace a faɗin kasar nan a zango na biyu na shekarar 2026 (wato Q2 2026).

Hedkwatar Tsaron Nijeriyar ta ce dakarunta sun kashe ’yanta’adda 662 da sauran gungun masu laifi, sun kama mutane 1,084 da ake zargi, kuma sun ceto mutane 951 da aka yi garkuwa da su a faɗin ƙasar a  zango na biyu na shekarar 2026.

Wannan ya biyo bayan yadda sojoji suka tsananta gudanar da samame bisa amfani da bayanan sirri domin daƙile hanyoyin sadarwa na ’yanta’adda da masu laifi.

Yayin da yake jawabi a wurin taron manema labarai a birnin Abuja a ranar Laraba, Daraktan Yada Labaran Hedkwatar Tsaron Nijeriya, Manjo Janar Michael Onoja, ya ce an samu waɗannan nasarori ne ta hanyar ɗorewar haɗin gwiwar samamen ƙasa, tallafin da aka samu daga sojojin saman ƙasar, da hadin gwiwa ta fuskar amfani da bayanan sirri.

A cewarsa, Rundunar Tsaron “ta samu gagarumar nasara mai girma a dukkan shiyyoyin ayyukanta a cikin watan Yuni da kuma Zango na Biyu na shekarar 2026.” Ya kuma bayyana cewa dakarun “sun kassara karfin gudanar da ayyuka na kungiyoyin Boko Haram, Daesh-WAP, haramtaccciyar kungiyar fafutukar kafa kasar Biafara (IPOB) da reshenta na makamai wato Eastern Security Network (ESN), da kuma gungun masu garkuwa da mutane, kungiyoyin satar danyen mai na haram, da masu safarar makamai ta kan iyakoki.”

Ya ce tarin nasarorin da aka samu na nuna “gagarumin kokari da sadaukarwa na kwararrun dakarun da suka kuduri aniyyar dawo da zaman lafiya, daidaito, da kwarin gwiwa a kowace shiyyar kasar.”

Onoja ya bayyana cewa shiyyar Arewa maso Gabas ta kasance cibiyar ayyukan soja a karkashin rundunar Operation Hadin Kai, inda dakarun suka kashe ’yanta’adda 484, suka kama mutane 370 da ake zargi, sannan suka ceto mutane 595 da aka yi garkuwa da su a cikin zango na biyun.

Ya kara da cewa shiyyar ta kuma shaida mika wuya na ’yantawaye 38 tare da iyalansu. Sannan daya daga cikin manyan samamen da aka gudanar ya kai ga ceto fararen-hula 360, wadanda akasarinsu mata ne da yara, yayin wani farmaki na hadin gwiwa da aka kai a tsaunin Mandara da ke Karamar Hukumar Gwoza a Jihar Borno.

A shiyyar Arewa maso Yamma kuma, dakarun da ke ƙarƙashin rundunar Operation Fansan Yamma sun kashe ’yanta’adda 77, sun kama mutane 210 da ake zargi, sannan sun ceto mutane 153 da aka yi garkuwa da su, yayin da suka yi nasarar kawar da masu safarar makamai, masu samar da kayan aiki, da masu hadin baki da ’yanta’adda a jihohin Kaduna, Katsina, Kebbi, da Zamfara.

“Hadin gwiwar ayyukan a shiyyar Arewa ta Tsakiya ya kuma jaddada irin muhimmancin da sojoji ke badawa wajen lalata kayayyakin more rayuwa na masu laifi,” in ji Onoja.

Ya bayyana cewa dakarun da ke aiki a karkashin rundunonin Operations Savannah Shield, Enduring Peace, da Whirl Stroke sun kashe ’yan ta’adda 83, sun kama mutane 305 da ake zargi, sannan sun ceto mutane 183 da aka yi garkuwa da su.

A cewarsa, “wasu samamen na musamman sun mayar da hankali ne kan masu kai wa ’yanta’adda bayanai, masu hadin baki da masu garkuwa da mutane, masu jigilar makamai na haram, da masu samar da kayan aiki, wanda hakan ya dagula hanyoyin tallafi da masu laifi ke amfani da shi na tsawon lokaci a yankin.”

A shiyyar Kudu maso Gabas kuwa, a karkashin rundunar Operation Udo Ka, sojoji sun kashe ’yanta’adda 12, sun kama mutane 115 da ake zargi, sannan sun ceto mutane 20 da aka yi garkuwa da su. Kazalika, ayyukan soji sun kai ga kwato makamai, bama-baman da aka kera da hannu, da harsasai, yayin da aka kama manyan kwamandojin IPOB/ESN da masu samar musu da kayan aiki a yayin samamen da aka kai musu hari na musamman.

Onoja ya ci gaba da cewa rundunar Operation Delta Safe da ke shiyyar Kudu maso Kudu ta mayar da hankali ne wajen yaki da zagon kasa ga tattalin arziki da shirya laifuka. Inda dakarun suka kashe masu laifi shida, suka kama mutane 84 da ake zargi, suka lalata haramtattun matatun mai guda 12, sannan suka kwato fiye da lita 464,268 na danyen mai da aka sace.

Ya ce adadin mutanen da aka kama ya zarce adadin ’yanta’addan da aka kashe a cikin zangon, inda ya bayyana cewa wadanda aka kaman sun hada da masu hadin baki da ’yanta’adda, masu ba su bayanai, masu daukar nauyinsu, masu samar musu da kayan aiki, masu safarar makamai, da mambobin kungiyoyin garkuwa da mutane. Wannan na nuna yadda sojoji suka kara kaimi wajen tarwatsa hanyoyin tallafawa masu laifi.

Ya sake jaddada cewa rundunar soji za ta ci gaba da gudanar da ayyukan yaki da ta’addanci, yaki da fashi da makami, yaki da garkuwa da mutane, yaki da satar mai, da kuma yaki da yaduwar makamai ba bisa ka’ida ba, domin kara dawo da zaman lafiya da tsaro a fadin kasar.