‘Yansandan Dubai sun ce sun rufe shafukan sada zumunta guda 103 na bogi a watanni uku da suka wuce a wani yunƙuri na yaƙi da zamba ta yanar gizo da kuma ƙarfafa tsaro a intanet.
An sanar da alkaluman ne a lokacin wata bita da Babban Sashen Binciken Laifuka ya gudanar, inda manyan jami’ai suka tantance yanayin laifuka da kaifin aiki da matakan daƙile barazanar tsaro da ke tasowa.
A cewar ‘yansandan Dubai, Mataimakin Babban Kwamandan Harkokin Laifuka Manjo Janar Hareb Al Shamsi ne ya jagoranci taron, wanda ya ce magance matsalolin zamba da ke kara tsananta na bukatar hadin gwiwa tsakanin jami’an tsaro, cibiyoyin gwamnati da kuma al’umma.
Ya bukaci mazauna yankin da kada su bayar da bayanan sirri ko na banki ga mutane ko shafukan da ba a tabbatar da sahihancin su ba, sannan su bayar da rahoton duk wani yunkurin zamba cikin gaggawa.
Mayar da hankali ga zamba a intanet
Jami’ai sun kuma yi bitar shari’o’in da Cibiyar Yaƙi da Zamba ke gudanarwa, suna duba dabarun da masu aikata laifuka ta intanet ke amfani da su da kuma tattauna hanyoyin inganta gano zamba da wuri da kuma ƙarfafa ƙarfin magance su.
Bitar ta ƙunshi ayyukan da ƙwararrun sassan bincike suka gudanar, inda ‘yansanda suka nuna ƙoƙarin faɗaɗa ayyukansu masu himma, haɓaka shirye-shiryen aiki da kuma kawar da aikata laifuka tun kafin su faru.
‘Yansandan Dubai sun ce bayanan laifuka na watanni uku na farkon shekara sun nuna raguwa a cikin wasu alamomi da dama na laifuka, suna danganta yanayin da ci gaba da aiwatar da ayyuka da matakan tsaro na riga-kafi.

















