Ministan Tsaron Isra’ila Israel Katz ranar Asabar ya ce ƙasarsa da haɗin gwiwar Amurka sun kai “hare-haren kandagarki” a Iran, saboda abin da ya kira barazanar da take yi ga tsaron ƙasarsu.
Kazalika Katz ya ayyana dokar ta-ɓaci ta ƙasa baki ɗaya, sannan ya yi kira ga ‘yan ƙasar su bi umarnin rundunar soji ta Home Front Command wadda ke da alhakin kare fararen-hula.
“Ƙasar Isra’ila ta kai harin kandagarki a Iran. Ministan Tsaro Israel Katz ya ayyana dokar ta-baci ta musamman a duka ƙasar,” a cewar wata sanarwa daga ma’aikatar tsaron ƙasar.
Ganau sun ce sun ji manyan ƙararraki na fashewar abubuwa a Tehran, inda hayaƙi ya mamaye sararin samaniya, ko da yake kawo yanzu Iran ba ta yi martani ba.
An ji ƙarar fashe-fashe a Isfahan, Qom, Karaj da Kermanshah, a cewar kamfanin dillanacin labarai na Fars News Agency.
Hare-haren na zuwa ne a yayin da ake tattaunawa tsakanin Amurka da Iran sakamakon zaman ɗarɗar kan shirin Iran na mallakar makaman nukiliya.
Rundunar sojin Isra’ila ta fitar da sanarwa inda ta yi kira ga ‘yan ƙasar su yi kaffa-kaffa, tana mai gargaɗi game da yiwuwar hare-hare na makamai masu linzami.














