Birnin Dakar ya rikide zuwa filin biki da annashuwa yayin da dubban ‘yan ƙasa suka fito kan tituna domin tarbar zakarun nahiyar Afirka, tawagar “Zakunan Teranga”, bayan nasarar da suka samu a gasar AFCON 2025, abin da ya nuna irin ƙauna da alfahari da al’ummar Senegal ke yi wa ƙungiyarsu.

‘Yanwasan Senegal sun yi faretin nasara a cikin bas mai buɗe rufi, suna nuna kofin ga jama’a yayin da dubban magoya baya suka rera waƙoƙi, suka busa vuvuzela, suka kuma cika manyan tituna har zuwa fadar shugaban ƙasa. 
Shugaba Bassirou Diomaye Faye ya yabawa tawagar bisa jajircewa da ƙarfin hali bayan sun doke Maroko da ci 1-0 a wasan ƙarshe a Rabat. Birnin ya cika da launukan kore, rawaya da ja, yayin da manya da yara suka yi murnar nasarar tarihi, wadda ta zama kofin AFCON na biyu a tarihin Senegal bayan na 2022.

















