Wasanni

Falconets ta Nijeriya ta lallasa New Caledonia da ci 10-1, ta kai zagayen gaba a gasar Kofin Duniya

Tawagar Nijeriyar ta mamaye wasan tun daga farko, inda ta ci 4-0 kafin a tafi hutun rabin lokaci, sun ƙara zura ƙwallaye shida bayan an dawo.

Newstimehub

Newstimehub

14 Sep, 2026

c3ce652f 4300 4365 b736 73d5667c1cfd 1789372107846

Tawagar ƙwallon kafa ta mata ta Nijeriya, Falconets, ta kai zagayen ‘yan-16 a gasar cin Kofin Duniya ta FIFA 2026 ta mata ‘yan ƙasa da shekara 20.

Hakan ya biyo bayan lallasawar da ta yi New Caledonia da ci 10-1 a Poland ranar Lahadi.

Tawagar Nijeriyar ta mamaye wasan tun daga farko, inda ta ci 4-0 kafin a tafi hutun rabin lokaci.

Bayan dawowa daga hutu, Falconets ta ƙara zura ƙwallaye shida.

Ramotalahi Kareem da Winner David sun zura ƙwallaye uku kowacce. Yayin da Rebecca Adegbemile ta ci ƙwallaye biyu, sai kuma Seimeyeha Akekoromowei da Tosin Rafiu suka ci ƙwallo ɗaya kowacce.

New Caledonia ta ci ƙwallo ɗaya daf da ƙarshen wasan, amma hakan bai hana Nijeriya samun gagarumar nasara ba.

Wannan nasara ta kai Falconets matsayi na biyu a rukunin F, tare da tabbatar da gurbinta na zuwa zagayen ‘yan-16.

A baya, tawagar ta Nijeriya ta tashi da 0-0 da China, bayan da Sifaniya ta doke ta da ci 2-0 a wasan farko.

Tawagar Siyafiya ce ke jagorantar rukunin da maki tara, kuma tuni ta samu gurbin zuwa zagayen ‘yan-16.

Ana sa ran Falconets za ta kara da Ingila a zagayen gaba.