Gabas Ta Tsakiya

Fidan ya yi gargadi kan amfani da Mashigar Teku ta Hormuz a matsayin makami a rikicin yankin

Ministan Harkokin Waje Hakan Fidan ya yi gargadin cewa tangarda ga hanyar na yin barazana ga zaman lafiyar yankin da tattalin arzikin duniya.

Newstimehub

Newstimehub

12 May, 2026

b322b9e0df7623eaebfa03df3a6b8a4fa2c163d3e1f94e3e75efd11e87d47ab8

Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Hakan Fidan a ranar Talata ya ce ‘Kar Mashigar Teku ta Hormuz ta zama makami, yana mai gargadin cewa tangarda ga hanyar na yin barazana ga zaman lafiyar yankin da tattalin arzikin duniya.

Da yake jawabi a wani taron manema labarai na hadin gwiwa da Firaministan Qatar kuma Ministan Harkokin Waje Mohammed bin Abdulrahman bin Jassim Al Thani a Doha, Fidan ya kuma ce ya zama lallai a tabbatar da tashin hankalin da ke ci gaba da faruwa a yankin Gulf “ba zai sa a manta da batun Gaza ba.”

Ya kuma yi gargadin cewa fadadar Isra’ila na ci gaba da zama babbar barazana ga “kwanciyar hankali da tsaro” na yankin.

Al Thani ya ce Qatar da Turkiyya suna goyon bayan kokarin shiga tsakani na Pakistan da nufin kawo karshen yakin Amurka-Isra’ila kan Iran da kuma sake bude mashigar Hormuz, yana mai jaddada bukatar dawo da kwanciyar hankali da kuma tabbatar da ‘yancin zirga-zirga ta hanyar mai matukar muhimmanci.

“Qatar da Turkiyya sun goyi bayan kokarin shiga tsakani na Pakistan don kawo karshen yaki kan ran da sake bude mashigar teku ta Hormuz,” in ji shi.

Ministan Harkokin wajen Qatar ya kuma ce bai kamata Tehran ta yi amfani da hanyar ruwa a matsayin hanyar “zalunci ko cin zarafi” ga kasashen Gulf ba.

Da yake jawabi kan Gaza, Al Thani ya zargi Isra’ila da ci gaba da keta yarjejeniyar tsagaita wuta da kuma “amfani da tallafin jinkai a matsayin makami” a yankin.

An yi taron manema labarai na hadin gwiwa a yayin ziyarar aiki da Fidan ya kai Doha babban birnin Qatar.