Wani mummunan hari da ya girgiza al’umma ya sake nuna irin halin da Sudan ke ciki, bayan da wani bam ya faɗa kan asibitin soji na Al-Kuweik a jihar Kudancin Kordofan. Harin ya yi sanadin rasa rayukan mutane da dama, ciki har da ma’aikatan jinya da ke aikin ceton rai, lamarin da ya jefa yankin cikin ƙarin tashin hankali da damuwa.
Ƙungiyar likitocin Sudan ta bayyana cewa akalla mutum 22 ne suka mutu yayin da wasu takwas suka jikkata, ciki har da daraktan asibitin da ma’aikatan jinya huɗu. Ƙungiyar ta zargi rundunar RSF da kai harin, tana mai bayyana hakan a matsayin laifin yaƙi da keta dokokin ƙasa da ƙasa da ke kare fararen-hula da cibiyoyin lafiya.
Rahoton ya ce harin ya tilasta rufe wasu asibitoci a jihar, lamarin da ya ƙara tsananta matsalar jinƙai da barazana ga rayukan fararen-hula. Ƙungiyar ta yi kira ga Majalisar Ɗinkin Duniya da ƙungiyoyin kare haƙƙin bil’adama da su ɗauki mataki cikin gaggawa domin dakatar da hare-hare kan wuraren jinya.
Rikicin da ke tsakanin sojojin Sudan da rundunar RSF tun daga Afrilun 2023 ya yi sanadin mutuwar dubban mutane tare da raba miliyoyin mutane da gidajensu, yayin da ƙasar ke ƙara nutsewa cikin rikicin jinƙai da tsaro.
Majiyar Labari: TRT HAUSA














