Rahotanni daga Najeriya sun tabbatar da cewa gwarzon ɗan damben boksin na Burtaniya ɗan asalin Najeriya, Anthony Joshua, ya gamu da hatsarin mota a jihar Ogun. Sai dai abin farin ciki shi ne, ba ya cikin wani hali mai muni, domin ya samu ƙananan raunuka ne kawai.
Hatsarin ya faru ne a kan hanyar Lagos–Ibadan, lokacin da motarsa ƙirar Lexus Jeep ta yi karo da wata babbar mota da aka ajiye a gefen titi. Rahotanni sun nuna cewa mutum biyu sun mutu a sakamakon lamarin, yayin da Joshua ya tabbatar wa ’yan sanda a Sagamu cewa yana cikin koshin lafiya.
Wasu hotuna da ke yawo a kafafen sada zumunta sun nuna motar da ta lalace, inda jaridar Punch ta wallafa hoton Joshua yana zaune a kujerar bayan motar.
Joshua dai yana Najeriya ne domin hutun ƙarshen shekara, bayan nasarar da ya samu a wasansa da Jake Paul a Miami, ranar 19 ga Disamba.














