Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ya yi watsi da ikirarin Amurka cewa Iran ta shirya kai hari kan Amurka ko dakarunta, yana mai cewa wannan zargi “karya ce tsantsa.” A cikin wani sako da ya wallafa a shafin X, Araghchi ya ce Iran ba ta shirya kai irin wannan hari ba.
Ya kara da cewa wannan zargi an kirkiro shi ne domin a ba da hujjar hare-haren soja da Isra’ila da Amurka suka kaddamar kan Iran, wanda ya kira wani “kuskuren yaki” da Isra’ila ta jagoranta. A cewarsa, irin wadannan matakai na kara haddasa tashin hankali a yankin.
Rikicin yankin ya kara tsananta bayan hare-haren hadin gwiwa da Amurka da Isra’ila suka kai kan Iran tun daga makon da ya gabata, wanda rahotanni suka ce ya yi sanadin mutuwar sama da mutane 1,200 tare da jikkatar dubban wasu. A martani, Iran ta kai hare-hare da jirage marasa matuka da makamai masu linzami kan Isra’ila da wasu kasashe a yankin da ke dauke da sansanonin sojin Amurka.














