Gabas Ta Tsakiya

Iraniyawa suna zanga-zanga bayan Amurka da Isra’ila sun kashe Khamenei

Iraniyawa sun fantsama kan tituna inda suke gudanar da zanga-zanga tare da yin alini bayan Amurka da Isra’ila sun kashe Jagoran Addini na ƙasar Khamenei a harin da suka kai masa.

Newstimehub

Newstimehub

1 Mar, 2026

e771ebbcb1035080103aa4c0f8bef51915927a62985d4c15df14969c22e5f234

Zanga-zanga ta ɓarke ranar Lahadi a faɗin ƙasar Iran bayan sanarwar da aka fitar cewa Amurka da Isra’ila sun kashe Jagoran Addini Ali Khamenei a hare-haren soji da suka kai ƙasar.

Lamarin ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zaman zulumi kuma ya jawo kakausan martani daga cikin ƙasar Iran.

Tun da farko gidan talbijin na Iran ya tabbatar da mutuwar Khamenei a hare-haren Amurka da Isra’ila, inda ya bayyana cewa Jagoran Addini na “Juyin-juya-halin Musulunci ya yi shahada.”

Kazalika gwamnatin ƙasar ta sanar da makokin kwana 40 tare da bayar da hutun kwana bakwai.

8567dc00a683a84d6f422adf263b505edd706a860574f3bffb130e780c74193b

Kafofin watsa labaran Iran sun ce masu zanga-zangar da ke riƙe da tutocin ƙasar Iran sun taru a cibiyoyin zanga-zanga a biranen ƙasar inda suke bayyana alhininsu.

A Tehran, ɗaruruwan mutane sun taru a Dandalin Inkilap, inda suke riƙe da tutocin ƙasar da fastocin Khamenei, inda suka riƙa Allah wadai da Amurka da Isra’ila.

A birnin Qom, ɗaruruwan mutane sun taru a Hubbaren Hazrat Masume domin yin tur da hare-haren.