Manchester City ta fara ganawa da Paris Saint-Germain don zawarcin golansu Gianluigi Donnarumma, wanda ke son barin Paris.
City na tattaunawa da ɗan wasan ɗan asalin Italiya, duk da daidaitawa da shi ba zai zo da wahala ba, saboda yana da burin sauya kulob a bazarar nan.
Sai dai batun Man City ta iya ɗauko Donnarumma zai dogara ne kan ko ƙungiyar za ta iya sakin golanta Ederson.
Fabrizio Romano ya ce PSG za ta iya neman farashi da zai kai euro miliyan €50, duk da a zahiri ya yi tsada. Amma ya danganta da yadda suka sayar da Ederson.














