Ministan Harkokin Wajen Turkiyya, Hakan Fidan, zai karɓi Ministan Harkokin Wajen Nijeriya, Yusuf Tuggar, a birnin Ankara ranar Litinin, a wata ziyara ta diflomasiyya da ake sa ran za ta ƙarfafa alaƙar ƙasashen biyu a fannoni da dama.
Wannan ita ce ziyara ta farko da Tuggar zai kai Turkiyya tun hawansa muƙami, inda ake sa ran Fidan zai jaddada muhimmiyar rawar da Nijeriya ke takawa wajen wanzar da zaman lafiya da tsaro a Yammacin Afirka. Haka kuma za a tattauna batutuwan da suka shafi bunƙasa cinikayya, zuba jari, da buƙatun kamfanonin Turkiyya da ke aiki a Nijeriya.
Bangarorin biyu za su kuma mai da hankali kan:
- Haɗin kai a fannin soji da tsaro
- Yaƙi da ƙungiyoyin ta’addanci
- Kyautata hulɗa a Majalisar Ɗinkin Duniya, OIC da D-8
Tattaunawa Kan Gaza da Somalia
Ministan Turkiyya zai nemi ƙarfafa haɗin kai tsakanin Ankara da Abuja a cikin OIC–Arab League Gaza Contact Group domin:
- Tabbatar da tsagaita wuta mai ɗorewa a Gaza
- Inganta ayyukan jinƙai
- Goyon bayan warware rikicin Falasdinu ta hanyar ƙasashe biyu masu cin gashin kansu
Haka kuma, za a tattauna batun Somalia, inda Turkiyya da Nijeriya ke goyon bayan kare cikakken ‘yancin kan ƙasar da kuma mutunta dokokin kasa da kasa.
Bunƙasar Cinikayya Tsakanin Turkiyya da Nijeriya
A fannin tattalin arziki:
- Cinikayya tsakanin ƙasashen biyu ta kai $688.4m a watanni 11 na 2025
- Nijeriya ce babbar ƙawar kasuwancin Turkiyya a yankin Sahara a 2025
- Kamfanonin Turkiyya sama da 50 suna aiki a Nijeriya
- Jimillar kwangilolin Turkiyya a Nijeriya sun kai kusan $3bn
- Akwai haɗin gwiwa mai ƙarfi a fannin makamashi da gine-gine
Ilimi da Hulɗar Jama’a
A bangaren ilimi:
- Dalibai 199 ‘yan Nijeriya sun kammala karatu a Turkiyya tsakanin 1992–2023
- A halin yanzu, 149 na karatu a ƙarƙashin shirin guraben karatu na Turkiyya
An ƙulla alaƙar diflomasiyya tsakanin Turkiyya da Nijeriya tun ranar 9 ga Nuwamba, 1960, kuma wannan ziyara na nuni da ƙarin zurfafa dangantakar siyasa, tsaro da tattalin arziki tsakanin ƙasashen biyu.
Majiyar Labari: TRT HAUSA














