A wani yanayi da ya nuna ƙarfafa alaƙar ƙasashen biyu, Ministan Harkokin Wajen Turkiyya, Hakan Fidan, ya tarbi takwaransa na Nijeriya, Yusuf Maitama Tuggar, a birnin Ankara ranar Litinin, a ziyararsa ta farko zuwa ƙasar tun bayan naɗinsa, lamarin da ke nuna sabuwar manufa ta ƙara kusantar diflomasiyya da haɗin gwiwa tsakanin Turkiyya da Nijeriya.
An kafa alaƙar diflomasiyya tsakanin ƙasashen biyu tun ranar 9 ga Nuwamba, 1960, kuma cinikin da ke tsakaninsu ya kai dala miliyan 688.4 cikin watanni 11 na farkon shekarar 2025, inda Nijeriya ta zama babbar abokiyar kasuwanci ta Turkiyya a Afirka, musamman a bangaren makamashi.
Fiye da kamfanonin Turkiyya 50 ne ke aiki a Nijeriya da jarin da ya haura dala miliyan 400, yayin da ayyukan ‘yan kwangila suka kusan kai darajar dala biliyan 3. Haka kuma, haɗin gwiwa a fannin tsaro da yaƙi da ta’addanci na ci gaba da ƙarfafa, tare da tallafin karatu da ya amfanar da ɗaliban Nijeriya 199 tun 1992, yayin da 149 ke karatu a halin yanzu.














