Jihar Cross River ta tabbatar da sabon kamuwa da cutar COVID-19, shekaru bayan barkewar annobar a duniya. Ma’aikatar lafiya ta jihar ta fara bin diddigin mutanen da suka yi hulɗa da wani ɗan ƙasar China da aka kwantar a asibiti bayan gwaji ya nuna yana dauke da cutar.
Kwamishinan lafiya, Henry Ayuk, ya bayyana hakan a Calabar, inda ya ce wannan shi ne babban lamari na farko da aka samu tun shekarar 2022. Ya kara da cewa ana zargin mutumin ya kamu da cutar ne a cikin Najeriya bayan ya shafe kwanaki fiye da 14, sannan alamun cutar suka bayyana a ranar 10 ga Afrilu.
Gwamnatin jihar ta fara ɗaukar matakai, inda aka tura ma’aikatan lafiya zuwa yankin Akamkpa, inda mutumin ke zama da aiki, domin hana yaduwar cutar. Ayuk ya kuma bukaci jama’a su kasance cikin shiri da lura, amma su ci gaba da harkokinsu na yau da kullum, yana mai tabbatar da cewa jihar na da ƙarfin dakile yaduwar cutar.
Majiyar Labari: Channels News














