Matatar Dangote ta ce tana da isasshen man jirgi da za ta iya wadatar da bukatun “duniya”

Matatar Mai ta Dangote a Nijeriya mai ƙarfin tace gangar mai 650,000 a kowace rana tana da isasshen man jirgin sama da za ta iya fitarwa zuwa kasuwannin duniya baki ɗaya, in ji Babban Daraktan kamfanin, David Bird, a ranar Talata.
2 Jun, 2026
Farashin man fetur a Nijeriya ya tashi da kashi 643% a cikin shekaru uku — Rahoto

Tashin farashin na baya bayan nan ya faru ne daga kimanin N800 da ake sayar da litar man cikin ‘yan watannin da suka gabata zuwa N1,300 sakamakon tashin hankalin da ake yi a Gabas Ta Tsakiya, lamarin da ya janyo tsaiko a harkar samar da mai a duniya.
2 Jun, 2026
Wike ya ce kiwon shanu a cikin birnin Abuja batu ne na tsaron ƙasa

Wike, wanda ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa kai-tsaye da kafafen yaɗa labarai a ranar Litinin, ya ce wannan ƙalubale na buƙatar tattaunawa ta gaskiya da kuma samar da mafita mai ɗorewa.
1 Jun, 2026
Tinubu ya ba da damar ɗaukar jami’an tsare dazuka 1,000 sakamakon garkuwa da ɗaliban jihar Oyo

Shugaban ya kuma umarci wani birged na tsaro na musamman mai ƙwarewa sosai a ceto mutane ya matsa kaimi wajen tabbatar da an sako waɗanda aka sacen.
1 Jun, 2026

Tsayar da Obi ɗan takarar NDC ya sake share fagen fafatawar manyan ‘yan takara uku a Nijeriya

NAHCON ta ba da umarnin bincike kan wani abinci da mahajjata suka ƙi ci kan ‘rashin inganci’

Masu tayar da ƙayar baya 30,000 na rura wutar rashin tsaro a Nijeriya – Rahoton Amurka

‘Yanbindiga sun yi garkuwa da mutum 10 tare da kona gidan wani sarki a jihar Kwara a Nijeriya

Sojojin Nijeriya sun kashe ‘yanta’adda 12 da ƙwato makamai a Borno
22 May, 2026
Wa zai fafata da Tinubu? Jam’iyyun siyasar Nijeriya na zaɓen fitar da ‘yan takarar shugabancin ƙasar
Jam’iyyun siyasar Nijeriya fiye da 20 ne ke shirin fara gudanar da zaɓukan fidda gwani na shugaban ƙasa daga ranar Asabar don zaɓar ‘yan takararsu a zaben ƙasar da za a yi a watan Janairu na shekara mai zuwa.

22 May, 2026
Kotu ta soke jadawalin INEC game zabukan fitar da gwani da tsayar da ‘yantakara na 2027
Alƙalin kotun, Maishari’a Mohammed Umar ya soke wa’adin ranar 10 ga watan Mayu da INEC ta gindaya, wani wa’adi da ke buƙatar dukkan jam’iyyuu siyasa su miƙa rijistar dukkan mambobinsu a matsayin sharaɗi na samun damar shiga manyan zaɓuka.

22 May, 2026
Tinubu ba shi da shirin sauya sunan Nijeriya ko soke shari’ar Musulunci a arewa – Fadar gwamnati
“Babu wani shiri ko yunƙuri, na kusa ko na nesa, da shugaban ƙasa yake da shi na taɓa tsarin Shari’a a Arewa ko kuma sauya sunan ƙasar nan,” in ji sanarwar Bayo Onanuga.

21 May, 2026
Hukumar Alhazan Nijeriya ta kammala jigilar maniyyatan ƙasar zuwa Saudiyya
NAHCON ta sanar da cewa jirgin Max Air ne ya yi jigilar ƙarshe inda ya tashi da misalin ƙarfe 10:44 na safiyar Alhamis, 21 ga Mayun 2026 daga Filin Jirgin Sama na Gusau zuwa Saudiyya.

21 May, 2026
Wasu sun nemi na mutu saboda tallafin mai da canjin dala— Tinubu
Shugaban Nijeriya Bola Tinubu a ranar Laraba ya bayyana cewa wasu mutane da suka fi kowa amfana daga tsarin tallafin mai da tallafin dala suna fatan ya mutu, biyo bayan tsare-tsaren da ya gabatar lokacin da ya hau ƙaragar mulki a shekarar 2023.

20 May, 2026
NDLEA ta tarwatsa ƙungiyar masu hada miyagun ƙwayoyi ta Nijeriya da Mexico ta kama mutum 10
Shugaban hukumar, Mohamed Buba Marwa ya bayyana hakan a hedikwatar hukumar da ke Abuja, inda ya ce wannan aiki ya yi wa manyan ƙungiyoyin aikata laifukan ƙetare iyaka mummunar illa.

20 May, 2026
Sojojin Nijeriya ‘bakwai ne’ suka mutu a wani harin kwanton ɓauna na’yanta’adda a Jihar Sokoto
Akalla sojojin Nijeriya bakwai ne aka kashe a karshen makon da ya wuce a wani kwanton bauna da ake zargin ‘yanta’adda ne suka kai musu a yankin arewa maso yamma kusa da kan iyaka da Nijar.

20 May, 2026
An kashe shugabannin Daesh 175 a arewa maso gabashin Nijeriya a farmakin haɗaka da Amurka
Wata sanarwa da Daraktan Yaɗa Labarai na hedikwatar tsaron Nijeriya Manjo Janar Samaila Uba ya fitar a ranar Talata ta ce, “Zuwa ranar 19 ga Mayun 2026, binciken farko ya tabbatar da cewa an kawar da ‘yanta’addan Daesh akalla 175 daga fage daga.

18 May, 2026
An sace yara da manya 46 a hare-haren makarantu a kudancin Nijeriya
Elisha Olukayode Ogundiya, shugaban Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya a Jihar Oyo, ya tabbatar da cewa mutum 46 aka sace a hare-haren.

18 May, 2026
Rundunar Sojin Amurka da ke aiki a Afirka ta ƙara kai sabbin hare-hare kan ‘yanta’adda a Nijeriya
Tinubu ya ce dakarun Nijeriya sun yi aiki kafaɗa da kafaɗa da rundunar sojin Amurka a wani abin da ya kira aikin hadin gwiwa mai jarumta wanda ya yi babbar illa ga ‘yanta’addan.



