‘Yanbindiga sun kashe Kanar na sojin Nijeriya bayan ya ƙi amincewa su yi garkuwa da shi

Abdussalam Ude, wanda Kanar ne a rundunar sojin Nijeriya, ya yi turjiya ga maharan duk da cewa suna da yawa, lamarin da ya jawo maharan suka harbe shi har lahira.
29 Jul, 2026
Aƙalla mutane 14 ne suka mutu a wani hari da aka kai a jihar Benue ta Nijeriya, in ji jami’an yankin

Harin na baya-bayan nan ya faru ne a kauyen Efeyi da ke yankin Otukpo na jihar da sanyin safiyar ranar Talata, inda ‘yan bindiga suka kashe mutane 14 tare da raunata wasu da dama, in ji shugaban karamar hukumar Otukpo, Maxwell Ogiri ga Reuters.
29 Jul, 2026
‘Yanta’adda sun kashe aƙalla mutum 30 a wani ƙauye a Kaduna ta Nijeriya

Kungiyar Al’ummar Kudancin Kaduna (SOKAPU) ta tabbatar da kisan, inda ta bayyana lamarin a matsayin wata alama ta taɓarɓarewar tsaro a yankunan karkara a faɗin jihar.
28 Jul, 2026
Ana fargabar ɗalibai sun maƙale bayan da gini mai ɗakuna 90 ya rufta da su

Hukumomin sun ce ba san adadin waɗanda suka mutu ba kuma ba za a iya tantance waɗanda suka maƙale ba, yayin da ake aikin ceto.
27 Jul, 2026

Rundunar Sojin Nijeriya ta kama jami’in da ake zargi da sayar wa ‘yanta’adda kayan soji

Jami’in da ke kula da harkokin kuɗin ISWAP ya miƙa wuya —Rundunar Sojin Nijeriya

INEC za ta rufe rijistar masu zaɓe ranar Lahadi, ‘yan adawa na neman a tsawaita lokacin rijistar

Sojojin Nijeriya sun ce suna ƙoƙarin ceto shugaban ƙaramar hukumar Bungudu a Zamfara

Dangote na shirin samar da wurin ajiyar mai a Kamaru
24 Jul, 2026
An yi jana’izar manoma 26 da aka kashe a harin ‘yanbindiga a Jihar Zamfara a Nijeriya
Hukumomin yankin sun ce an kai wa manoman harin ne yayin da suke aiki a gonakinsu a Ƙaramar Hukumar Kaura Namoda ta Jihar Zamfara a ranar Alhamis.

24 Jul, 2026
Rundunar Sojin Nijeriya na neman jami’inta ruwa-a-jallo kan zargin sayar wa ‘yanta’adda kayan soji
A cikin wata sanarwa da rundunar sojin ta fitar, sunan sojan da ake nema Private Mohammed Yusuf Amutu, wanda ke aiki a sashen ɗinka inifam na sojin ƙasa na Nijeriya kafin ya tsere daga sansaninsa a ranar 3 ga Yunin 2026.

23 Jul, 2026
ICPC ta miƙa filin ginin gidaje 962 na aikin dala miliyan 65 ga Bankin Lamunin Gidaje na Nijeriya
ICPC ta ce an karɓi rancen dala miliyan 65 inda aka sayi filin domin aiwatar da aikin gina gidaje da bankin ya ƙaddamar a shekarar 2012.

23 Jul, 2026
Matatar Dangote ta koma sayar da fetur a naira, ta ƙara farashin lita da N140
Wannan na zuwa ne mako guda bayan matatar man ta Dangote ta dakatar da loda fetur ga manyan motoci tare da sauya tsarin biyan kuɗi zuwa dalar Amurka, matakin da ya jefa kasuwar man fetur cikin ruɗani.

22 Jul, 2026
Trump ya yabi Tinubu kan ‘jagorancinsa a yaƙi da ta’addanci’ a Nijeriya
A cikin wata wasiƙa mai ɗauke da kwanan watan 6 ga Yuli, 2026, Trump ya jinjina wa Tinubu bisa ƙudirinsa na magance matsalolin tsaro a Nijeriya, yana mai cewa Amurka na alfaharin tsayawa tare da Nijeriya a yaƙi da ta’addanci.

22 Jul, 2026
Nijeriya ta kaddamar da shirin takardun lamuni na N729bn don biyan basussuka a fannin lantarki
Ministan Kuɗi kuma Ministan Kula da Tattalin Arziki, Taiwo Oyedele, ne ya sanar da hakan yayin wani taron masu zuba jari da aka gudanar a Abuja.

22 Jul, 2026
An yi garkuwa da fiye da mutum 40 a hare-haren ‘yanbindiga a Jihar Zamfara
A cewar wani mazaunin gundumar Mayanchi da ke ƙaramar hukumar Maru, maharan sun kai hare-hare a ƙauyuka 11 tsakanin ranar Juma’a da Lahadi, inda suka kai farmaki al’ummomin Tashar Mayanchi, Gwargawo, Jidda da Garagi, da sauransu.

21 Jul, 2026
NESREA ta fara bincike kan zargin zubewar sinadari a babbar hanyar Kaduna-Abuja
Tawaga daga ofishin NESREA reshen Jihar Kaduna, ƙarƙashin jagorancin Kodinetan jihar, Hena Dangari Emmanuel, ta kai ziyara wurin domin tantance abin da ya faru tare da fara bincike.

21 Jul, 2026
Jami’an tsaron Nijeriya sun kama ɗanta’adda ɗan ƙasar Sudan da wata mace ‘yar Ghana a Borno
Dakarun da ke kai farmakan HADIN KAI sun kama wani dan kasar Sudan da ake zargi da zama dan ta’adda daga kasar waje, tare da wata mace ‘yan kasar Ghana a yankin Askira/Uba da ke jihar Bornon Nijeriya.

21 Jul, 2026
DSS ta Nijeriya za ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin ɗaurin rai da rai da aka yanke wa shugabannin Ansaru
Hukumar DSS ta Nijeriya ta soki hukuncin da aka yanke wa shugabannin Ansaru inda ta ce hukuncin bai dace da girman laifukan da suka aikata ba.



