Sabon rahoto daga rundunar sojojin Najeriya ya nuna ci gaba a kokarin inganta tsaro, bayan da dakarun suka gano tulin albarusai sama da 1,200 da aka boye a cikin kwata a unguwar Bulumkutu, Maiduguri, lamarin da ke tabbatar da cewa ana kara daukar matakai wajen kare al’umma da dakile barazanar ‘yan ta’adda.
Jami’in watsa labarai na Rundunar Hadin Kai ta Arewa maso Gabas, Laftanal Kanal Sani Uba, ya bayyana cewa ci gaba da kasancewar sojoji a yankin da bincike na musamman ya taimaka wajen gano makaman, domin hana ‘yan ta’adda samun damar sake tada fitina.
Rahoton ya bayyana cewa an gano albarusan a cikin wata magudanar ruwa, kuma an dauki matakan kare jama’a tare da tura ƙwararru masu kula da abubuwa masu fashewa. Rundunar ta ce ana ci gaba da kwashe ruwan da ke cikin kwatar domin duba ko akwai karin makamai.














