Yayin da hare-haren ta’addanci ke ƙara kamari a Mogadishu da yankunan da ke kewaye da birnin, Turkiyya ta ɗauki matakin ƙarfafa goyon bayanta ga Somaliya ta hanyar faɗaɗa tura sojojinta. Jami’an tsaron Turkiyya sun bayyana cewa an ƙara rundunonin sama da na ƙasa domin taimaka wa Somaliya wajen kare ƙasarta da kuma dakile barazanar tsaro.
A cewar jami’an, Rundunar Haɗin Gwiwar Somaliya da Turkiyya tare da Sashen Rundunar Sojin Sama na Turkiyya suna ci gaba da inganta ƙarfin Somaliya ta hanyar tallafin soja, horo da ayyukan ba da shawara. An kuma ƙarfafa Rundunar Sojin Saman Turkiyya da ke Somaliya da ƙarin sojoji da kayan aiki domin ci gaba da yaƙi da ta’addanci.
Somaliya dai ta shafe sama da shekaru goma tana fama da ƙungiyar al-Shabaab mai alaƙa da al-Qaeda, wadda ke kai hare-hare ta bama-bamai da kisan kai duk da ayyukan soji da dakarun Somaliya, Tarayyar Afirka da ƙasashe ƙawaye ke yi. A ‘yan watannin nan, ƙungiyar ta ƙara kai hari kan hukumomin gwamnati da wuraren taron jama’a.
Turkiyya na daga cikin manyan abokan Somaliya, inda take da babban sansanin horar da soji a Mogadishu tare da horar da dubban sojoji da samar da kayan aiki da taimakon fasaha. Ankara ta ce burinta shi ne taimaka wa Somaliya gina tsarin tsaro mai ɗorewa domin samun zaman lafiya na dogon lokaci da rage dogaro da ƙasashen waje.
Majiyar Labari: TRT AFRIKA

















