An sake samun rahoton rasuwar wani fursunan Falasɗinu a hannun hukumomin Isra’ila, lamarin da ke ƙara janyo cece-kuce kan halin da ake ciki a gidajen yari. Rahotanni daga kafafen yaɗa labarai na Falasɗinu sun tabbatar da mutuwar Hassan Issa al-Qasha’leh, ɗan asalin birnin Rahat da ke yankin Negev.
A cewar hukumar labarai ta Falasɗinu WAFA, al-Qasha’leh ya rasu ne a ranar Alhamis a cikin Gidan Yarin Beersheba da ke kudancin Isra’ila. Rahoton ya nuna cewa ya shafe fiye da watanni 13 a tsare, kuma ana sa ran sakin sa bayan watanni shida masu zuwa.
Tun da farko, Hukumar Kula da Gidajen Yari ta Isra’ila ta tabbatar da mutuwar wani fursunan Falasɗinu da ake tsare da shi ba tare da shari’a ba, amma ba ta bayyana sunansa ba. Hukumar ta ce an kafa kwamitin bincike na musamman, kuma har yanzu ba a tantance musabbabin mutuwar ba.
Mutuwar ta zo ne a daidai lokacin da ake samun ƙaruwa a rahotannin da ke nuna tabarbarewar yanayi a gidajen tsare Falasɗinawa a Isra’ila.
Ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam na Falasɗinu sun yi gargadi cewa dubban Falasɗinawa na tsare cikin mawuyacin hali, inda suke zargin ana aikata cin zarafi iri-iri da suka haɗa da rashin kulawar lafiya, tsangwama, yunwa da kuma cin mutunci.
A cewar Ofishin Yaɗa Labarai na Fursunonin Falasɗinu, manufofin killacewa, danniya da sakaci da gangan suna barazana ga lafiyar fursunoni tare da rage juriyarsu a zaman yari. Ofishin ya ɗora alhakin kare lafiyar fursunoni gaba ɗaya kan Isra’ila, yana kuma kira da a ɗauki matakin gaggawa na shari’a da jin ƙai.
Hukumomin Falasɗinu sun kiyasta cewa fiye da Falasɗinawa 9,300 ke tsare a gidajen yari na Isra’ila a halin yanzu, ciki har da mata sama da 50 da kuma yara kusan 350. Wadannan alkaluma ba su haɗa da waɗanda ake tsare da su a sansanonin sojojin Isra’ila ba.
Tun daga watan Oktoba 2023, ƙungiyoyin Falasɗinu sun ce akalla fursunoni 100 ne suka mutu a tsare a gidajen yarin Isra’ila.














