Nijeriya

‘Yanta’adda sun sace fiye da mutum 300 a Jihar Bornon Nijeriya, in ji hukumomi

An kuma kai wasu hare-hare a kan al’ummomin Konduga, Marte, Jakana da Mainok tsakanin Laraba da safiyar Jumma’a, in ji kakakin rundunar soji Uba Sani.

Newstimehub

Newstimehub

6 Mar, 2026

877857eec9d83c77b5f8b7828f880aadc509fcc192165e81ff39a71bead8f999

Wasu ‘yanbindiga sun kai hari wani gari a arewa-maso-gabashin Nijeriya, inda suka sace fiye da mutum 300, ciki har da mata da yara, a ranar Jumma’a, in ji jami’an yankin.

Harin ya faru ne a garin Ngoshe a Jihar Borno, in ji Bulama Sawa, wani jami’i daga yankin Gwoza. Ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AP cewa harin na iya zama martani ga wani aikin soji da ya kashe kwamandoji uku na kungiyar ‘yanta’adda ta Boko Haram.

An kuma kai wasu hare-hare a kan al’ummomin Konduga, Marte, Jakana da Mainok tsakanin Laraba da safiyar Jumma’a, in ji kakakin rundunar soji Uba Sani.

Uba Sani ya ce dakarun sun samu nasarar tarwatsa hare-haren a Konduga, Marte, Jakana da Mainok, amma wasu jaruman sojoji sun rasa rayukansu a yayin aikin, tare da wani babban jami’i. Sai dai bai yi ƙarin bayani kan adadin sojojin da suka rasa rayukansu ba.

Sani ya bayyana hare-haren a matsayin “hare-haren da ba su yi nasara ba” da kuma “ƙaruwar matsin lamba kan ‘yan ta’addan saboda ci gaba da hari da ake kai musu a fadin yankin.”