Ministocin harkokin wajen ƙasashen NATO sun gudanar da taro domin tattaunawa kan yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin Rasha da Ukraine, da kuma tsare-tsare na ƙarfafa tsaro a ƙasashen mambobin ƙungiyar. A jawabinsa na buɗe taro, shugaban NATO Mark Rutte ya zargi Rasha da shirya faɗa mai ɗorewa tare da keta dokar kiyaye hurumin ƙasashen duniya a sararin samaniya.
Rutte ya kuma ce Rasha na aiki kafa ɗaya da China, North Korea da Iran wajen ƙoƙarin lalata tsaro da raba kan ƙasashen duniya kan dokokin ƙasa da ƙasa. Ya jaddada cewa dole ne ƙasashen NATO su dage kan haɗin kai da nuna ƙarfin gwiwa domin kare tsaro da muradun ƙasashen mambobin ƙungiyar.














