Najeriya Duniya Tattalin Arziki

Jersey za ta mayar wa Najeriya dala miliyan $9.5 da aka kwato domin aikin titin Abuja–Kano

Gwamnatin Jersey ta amince da mayar wa Najeriya sama da dala miliyan $9.5 da aka kwato daga kudaden cin hanci, domin tallafa wa aikin titin Abuja–Kano.

Newstimehub

Newstimehub

10 Jan, 2026

HM Attorney General for Jersey. Mark Temple KC signing MOU with Nigeria December 2025 v3 e1767958030950 750x375 1 700x350 1

Ƙasar Jersey tare da Gwamnatin Tarayyar Najeriya sun kammala shirye-shiryen mayar da sama da dala miliyan $9.5 da aka gano a matsayin kudaden cin hanci, inda aka amince a yi amfani da su wajen kammala aikin titin Abuja–Kano.

An cimma wannan matsaya ne ta hanyar yarjejeniyar fahimtar juna (MoU) da Babban Lauyan Jersey, Mark Temple KC, ya sanya wa hannu a watan Disambar 2025. Yarjejeniyar ta ba da damar tura kudin zuwa Najeriya domin amfani da su a aikin titin tarayya mai tsawon kilomita 375 da ke haɗa Abuja da Kano.

Kwato kudaden ya biyo bayan hukuncin Kotun Royal ta Jersey a ranar 12 ga Janairu 2024, bayan bincike ya nuna cewa kudaden sun samo asali ne daga karkatar da dukiyar jama’a ta hannun ‘yan kwangila da ke aiki don amfanin manyan jami’an Najeriya da abokan hulɗarsu.

Wannan ba shi ne karon farko ba da Jersey ke mayar wa Najeriya kudaden da aka kwato, domin a yarjejeniyoyi da suka gabata, an riga an dawo da sama da dala miliyan $300 da aka yi amfani da su wajen manyan ayyukan more rayuwa kamar titin Lagos–Ibadan da Gadar Neja ta Biyu.

Babban Lauyan Tarayyar Najeriya kuma Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi (SAN), ya bayyana matakin a matsayin hujja ta ƙoƙarin Najeriya wajen haɗa kai da ƙasashen duniya domin yaƙi da cin hanci, yana mai tabbatar da cewa za a yi amfani da kudaden yadda yarjejeniyar ta tanada.

Majiyar Labari: TVC NEWS