Hukumar diflomasiyyar Nijeriya ta tabbatar da cewa an warware matsalar da ta taso tsakaninta da Burkina Faso bayan jirgin dakon kayan sojojin Nijeriya ya yi saukar gaggawa saboda matsalar na’ura.
Ministan harkokin wajen Nijeriya, Yusuf Tuggar, ya ce bayan tattaunawar da aka yi cikin lumana tsakaninsa da shugaban Burkina Faso Ibrahim Traoré, an fahimci juna tare da bullo da mafita. A cewar mai magana da yawunsa, Alkasim Abdulkadir, bangarorin biyu sun tattauna cikin natsuwa tare da cimma matsaya mai kyau.
Rahoton ya nuna cewa an tsare sojojin kusan makonni biyu da suka gabata bayan kungiyar AES ta bayyana saukar jirgin a matsayin sabawa ka’idojin kasa da kasa. Sai dai rundunar sojin saman Nijeriya ta ce jirgin ya yi saukar gaggawa ne a Bobo-Dioulasso saboda matsalar na’ura, kuma matakin ya kasance na tsaro da doka.
Ko da yake akwai rahotannin da ke cewa an riga an saki sojoji 11, minista Tuggar ya ce har yanzu ba a saki su gaba ɗaya ba, amma komai yana kan hanya kuma ana sa ran matsalar za ta kare nan ba da jimawa ba.
Tattaunawar sulhun ta mayar da hankali kan karfafa hadin kai, tsaro, siyasa da tattalin arziki tare da tabbatar da kyakkyawar alaka tsakanin kasashen biyu.














