Bayan makonni na jayayya da tattaunawar diflomasiyya, jirgin saman sojin Nijeriya kirar C-130 da aka tsare a Burkina Faso ya ƙaura zuwa ƙasar Portugal, inda ake sa ran za a yi masa cikakken gyara.
Rundunar Sojin Saman Nijeriya ta tabbatar da cewa jirginta kirar C-130, wanda ya yi saukar gaggawa a Burkina Faso sakamakon matsalar na’ura, yanzu ya isa ƙasar Portugal domin a yi masa gyara.
A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, Air Commodore Ehimen Ejodame, ya fitar a yammacin ranar Juma’a, ya ce jirgin ya “isa wurin gyara na OGMA da ke birnin Lisbon, Portugal cikin aminci.” Ya ƙara da cewa matuƙan jirgin da sauran sojojin da ke cikinsa suna cikin ƙoshin lafiya.
Jirgin ya tashi ne daga birnin Banjul na ƙasar Gambia, inda ya samu taimakon wani jirgin ɗaukar kaya kafin ya ci gaba da tafiya zuwa Portugal domin gyara.
Tun a farkon watan Disamba ne jirgin dakon kaya na rundunar sojin saman Nijeriya, ɗauke da sojoji 11, ya yi saukar gaggawa a birnin Bobo Dioulasso na Burkina Faso sakamakon matsalar na’ura. Daga bisani, hukumomin Burkina Faso suka tsare jirgin tare da sojojin da ke cikinsa.
Ƙungiyar AES, wadda ta ƙunshi Burkina Faso, Mali da Nijar, ta yi ikirarin cewa an tilasta saukar jirgin ne saboda ya shiga sararin samaniyar Burkina Faso ba tare da izini ba. Lamarin ya jawo taƙaddamar diflomasiyya tsakanin ƙasashen biyu.
Daga ƙarshe, Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya aike da Ministan Harkokin Wajen ƙasar, Yusuf Tuggar, zuwa Burkina Faso domin gana wa da Shugaban ƙasar, Kyaftin Ibrahim Traore. Wata sanarwa daga ofishin ministan ta tabbatar da cewa an warware matsalar cikin lumana, inda aka saki jirgin da sojojin Nijeriya.














