A hakikanin gaskiya wannan labarin ya sake hargitsa tattaunawar zaman lafiya a Sudan, domin shugaban Majalisar Mulkin Soji, Abdel Fattah al-Burhan, ya ce gwamnati ba za ta amince da kowace yarjejeniya ko tsagaita wuta ba muddin mayakan ’yan tawaye na cigaba da kasancewa a sassan ƙasar. Ya jaddada cewa zaman lafiyar gaskiya zai samu ne kawai bayan dawowar cikakken ikon gwamnati a duk faɗin Sudan.
Al-Burhan ya bayyana haka ne a Ankara yayin ganawa da shugabannin al’umma, wakilan kungiyoyin farar hula da ’yan jarida. Ya ce shirin zaman lafiyan da Firaminista Kamil Idris ya gabatar wa Majalisar Dinkin Duniya shi ne hangen nesan gwamnati guda ɗaya domin kawo ƙarshen rikicin. Ya kuma ce Majalisar Mulki da Majalisar Ministoci sun amince da shirin tare da shirin ƙarin tattaunawa don tabbatar da aiwatar da shi.
Duk da wannan matsayi, Burhan ya ce gwamnati ba ta neman yaƙi, amma so take a mutunta ikon ƙasa. Ya kira masu kira da a yi sulhu da ’yan tawaye da su yi musu shawara su mika wuya. Ya kuma bayyana goyon bayan Sudan ga manufofin Saudiyya da Masar wajen samar da mafita. Haka kuma ya jaddada cewa Sudan ba ta kai wa makwabta hari, sai dai tana da ’yancin kare kanta.
Al-Burhan ya kuma yaba da dangantakar Sudan da Turkiyya, yana kiran ta “dangantaka ta tarihi da haɗin gwiwa mai ma’ana.” Wannan ya zo ne bayan ganawarsa da Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan inda suka tattauna dangantakar ƙasashen biyu da ci gaban yankin.














