Rahotanni daga Syria sun nuna cewa kungiyar YPG ta kwace iko da Asibitin Yassin da ke unguwar Sheikh Maqsoud a birnin Aleppo, inda ta kori likitoci da sauran ma’aikatan lafiya tare da mayar da asibitin sansanin soja.
Ma’aikatar Lafiya ta Syria, a wata sanarwa da Kamfanin Dillancin Labarai na ƙasar SANA ya wallafa, ta ce ‘yan kungiyar PKK da ke da alaƙa da YPG sun tilasta wa ma’aikatan asibitin ficewa bayan sun tsere gaban Rundunar Sojan Syria. Hukumomin sun gargadi fararen hula da su nisanci yankin saboda barazanar tsaro.
A wani bangare, majiyoyin soji sun ce wani ɗan kungiyar YPG ya kai harin kunar-baƙin-wake kusa da rundunar soji a Sheikh Maqsoud, amma ba a samu asarar rai ba. Rundunar Sojan Syria ta bayyana cewa ta kammala share yankin tare da tabbatar da tsaro.
Hare-haren da aka ce kungiyar YPG ta kai a unguwannin Aleppo sun kashe mutane tara, sun jikkata fiye da 50, tare da tilasta wa dubban mazauna yankin barin gidajensu. Hukumomi sun ce duk da yarjejeniyar da aka kulla a watan Maris domin haɗa ƙungiyar cikin hukumomin gwamnati, YPG ba ta cika sharuddan da aka amince da su ba.














