Gabas Ta Tsakiya

Trump Ya Yi Barazanar Ɗaukar Mataki Mai Tsauri Kan Iran Saboda Hukuncin Rataye Masu Zanga-zanga

Shugaban Amurka Donald Trump ya gargaɗi Iran da cewa za ta fuskanci tsattsauran mataki idan ta fara aiwatar da hukuncin kisa kan masu zanga-zanga.

Newstimehub

Newstimehub

14 Jan, 2026

1768368358359 kqfpt f1fa125c79929c8ff7283c4d61c1e081252ed3c0ee444b4f3f167654e589b21b e1768413103365

Shugaban Amurka Donald Trump ya yi gargaɗin cewa gwamnatinsa za ta ɗauki mataki mai tsauri idan hukumomin Iran suka fara rataye masu zanga-zanga, yana mai cewa hakan zai zama abin da ba za a lamunta ba.

Da yake magana da tashar CBS News, Trump ya ce Amurka ba za ta zauna ta kalli yadda ake kashe masu bore ba, musamman bayan da Tehran ta fara shirin gurfanar da wasu a gaban kotu bisa zargin “moharebah” – wato yaƙi da Allah.

Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta ce an riga an yanke wa wani matashi mai suna Erfan Soltani hukuncin kisa, tana mai gargadin cewa hakan na iya zama farkon jerin hukuncin rataye.

A martaninta, Iran ta zargi Washington da ƙoƙarin shirya hujjar kai farmaki na soja, tana mai cewa barazanar Trump ba za ta yi tasiri ba.

Kungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam sun ruwaito mutuwar daruruwan mutane da kuma tsare fiye da 10,000, yayin da hukumomin Iran ke cewa sun maido da doka da oda bayan zanga-zangar da ta girgiza ƙasar.

Majiyar Labari: TRT HAUSA