Shugaban Amurka Donald Trump ya yi gargaɗin cewa gwamnatinsa za ta ɗauki mataki mai tsauri idan hukumomin Iran suka fara rataye masu zanga-zanga, yana mai cewa hakan zai zama abin da ba za a lamunta ba.
Da yake magana da tashar CBS News, Trump ya ce Amurka ba za ta zauna ta kalli yadda ake kashe masu bore ba, musamman bayan da Tehran ta fara shirin gurfanar da wasu a gaban kotu bisa zargin “moharebah” – wato yaƙi da Allah.
Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta ce an riga an yanke wa wani matashi mai suna Erfan Soltani hukuncin kisa, tana mai gargadin cewa hakan na iya zama farkon jerin hukuncin rataye.
A martaninta, Iran ta zargi Washington da ƙoƙarin shirya hujjar kai farmaki na soja, tana mai cewa barazanar Trump ba za ta yi tasiri ba.
Kungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam sun ruwaito mutuwar daruruwan mutane da kuma tsare fiye da 10,000, yayin da hukumomin Iran ke cewa sun maido da doka da oda bayan zanga-zangar da ta girgiza ƙasar.














