Yayin da rikicin rabon ruwan Kogin Nilu ke ci gaba da janyo hankalin duniya, shugabannin Masar da Sudan sun nuna fatan cewa shiga tsakani da Shugaban Amurka Donald Trump ya yi zai iya kawo sabuwar dama ta warware takaddamar da ke tsakaninsu da Habasha kan gagarumin madatsar ruwan GERD.
Shugaban Masar Abdel Fattah al-Sisi da shugaban Sudan Abdel Fattah al-Burhan sun bayyana goyon bayansu ga tayin Trump na sasanta rikicin dam ɗin GERD. Sisi ya bayyana Nilu a matsayin “tushen rayuwar al’ummar Masar” tare da jaddada bukatar hadin gwiwa bisa dokokin kasa da kasa don kare tsaron ruwan Masar. Burhan ma ya ce Sudan na maraba da shirin, yana fatan zai kai ga yarjejeniya mai dorewa wadda za ta kiyaye haƙƙin kowane bangare da zaman lafiyar yankin.
Rikicin ya samo asali ne daga ginin madatsar ruwan GERD da Habasha ta kammala a 2025, inda Masar da Sudan ke neman yarjejeniya ta doka kan cika da amfani da dam ɗin.














