Ambaliyar ruwa da ta addabi ƙasar Mozambique ta haifar da wani mummunan haɗari, inda kada suka fara bayyana a cikin garuruwa da ƙauyuka da ruwa ya mamaye, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar aƙalla mutane uku.
A birnin Xai-Xai, babban birnin lardin Gaza, hukumomi sun gargaɗi jama’a da su yi taka-tsantsan, bayan da matakan kogin Limpopo suka tashi suka kutsa cikin yankunan da mutane ke zaune. Ana ci gaba da kwashe jama’a zuwa wurare masu tsayi domin guje wa haɗarin ambaliya da na namun daji.
Ruwan sama mai ƙarfi da ambaliya a Kudancin Afirka cikin wata guda sun kashe sama da mutane 100 a Mozambique, Afirka ta Kudu da Zimbabwe, tare da lalata dubban gidaje, hanyoyi, gadoji, makarantu da cibiyoyin lafiya.
A cewar hukumomi, daga cikin mutane 13 da suka mutu sakamakon ambaliya a Mozambique, uku kada ne suka kashe su.
Shugabar ofishin MDD mai kula da ayyukan jin-ƙai a Mozambique, Paola Emerson, ta ce tashin matakin ruwa ya sa kada daga kogin Limpopo suka samu damar shiga unguwanni da ruwa ya mamaye.
“Matakin koguna na tashi zuwa cikin birane, kuma wannan na bai wa kada damar shiga wuraren da mutane ke zaune,” in ji ta.
Rahotanni sun ce wasu kada sun shigo ne daga wani gandun daji a Afirka ta Kudu sakamakon ambaliya, inda a garin Moamba wani mutum ya fada bakin kada har ya hadiye shi.
Hukumomi sun yi kira ga jama’a da su guji kusantar ruwan da ba ya gudu, suna mai cewa kada na yawo a ciki kuma haɗarin yana da matuƙar girma.














