A wani muhimmin mataki na kare tsaro, Rundunar ’Yansandan Nijeriya ta kama wata babbar mota da ake zargin tana ɗauke da abubuwan fashewa a garin Saki na Jihar Oyo, kudu maso yammacin ƙasar. An gano motar ne bayan jami’an tsaro sun kafa shingen bincike bisa sahihan bayanan sirri.
A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar a jihar, Ayanlade Olayinka, ya fitar, ya bayyana cewa Kwamishinan ’Yansandan Jihar Oyo, Femi Haruna, ya bayar da umarnin a fara cikakken bincike kan kayayyakin da aka kama. Tuni ƙwararru suka fara tantance irin abubuwan domin tabbatar da nau’insu da haɗarinsu.
Direban motar ya shiga hannun hukuma, kuma yana bayar da haɗin kai ga masu bincike domin gano cikakken bayani kan inda aka fito da kayan da kuma inda ake shirin kai su. Rundunar ta jaddada cewa ana ci gaba da aiki da bayanan sirri don dakile duk wata barazana ga tsaron jama’a.
Kwamishinan ’Yansandan ya yaba da jagorancin Babban Sufeto Janar na ’Yansandan Nijeriya, Kayode Egbetokun, kan yadda yake ƙarfafa amfani da bayanan sirri wajen yaki da laifuka a fadin ƙasar.
Majiyar Labari: TRT HAUSA














