Ministar Lafiya ta Faransa, Stéphanie Rist, ta bayyana cewa gwamnati na da burin fara binciken ciwon huhu ga jama’a baki ɗaya nan da shekarar 2030. Ta ce a halin yanzu babu tsarin bincike na gama-gari kamar yadda ake yi wa ciwon nono ko na hanji, amma ana shirin samar da irin wannan tsari domin gano ciwon huhu da wuri.
A cewarta, matakin farko zai fara ne tun watan Maris, inda sama da mutane 20,000 za su shiga bincike na musamman a matakin gwaji.Ministar ta kara da cewa shigar da marasa lafiya cikin bincike da gwaje-gwaje daban-daban zai taimaka wa gwamnati tantance wa waɗanne ’yan ƙasa ya kamata a rika yi wa gwajin, domin a kai ga cikakken tsarin kasa baki ɗaya nan da 2030.
Ta kuma ce Shugaban ƙasa Emmanuel Macron zai bayyana matakai da kudaden da za a ware a cikin dabarar yaki da cutar kansa ta kasa na shekarun 2020 zuwa 2030. A cewar National Cancer Institute (INCa), ciwon huhu na ci gaba da zama mafi kisa a Faransa, da sabbin marasa lafiya kusan 52,000 a duk shekara, tare da kusan mutuwar mutane 33,000, inda rahotannin Santé publique France ke nuna cewa mace-macen na raguwa a maza amma na karuwa a mata sakamakon shan taba.
Majiyar Labari: AA














