Duniya Kimiyya Da Fasaha Lafiya

Faransa Na Shirin Kaddamar Da Gabaɗayan Binciken Ciwon Huhu Zuwa 2030

Gwamnatin Faransa na shirin fara binciken ciwon huhu ga jama’a baki ɗaya nan da 2030, tare da matakin farko da zai fara a watan Maris domin gano cutar da wuri.

Newstimehub

Newstimehub

4 Feb, 2026

download 1

Ministar Lafiya ta Faransa, Stéphanie Rist, ta bayyana cewa gwamnati na da burin fara binciken ciwon huhu ga jama’a baki ɗaya nan da shekarar 2030. Ta ce a halin yanzu babu tsarin bincike na gama-gari kamar yadda ake yi wa ciwon nono ko na hanji, amma ana shirin samar da irin wannan tsari domin gano ciwon huhu da wuri.

A cewarta, matakin farko zai fara ne tun watan Maris, inda sama da mutane 20,000 za su shiga bincike na musamman a matakin gwaji.Ministar ta kara da cewa shigar da marasa lafiya cikin bincike da gwaje-gwaje daban-daban zai taimaka wa gwamnati tantance wa waɗanne ’yan ƙasa ya kamata a rika yi wa gwajin, domin a kai ga cikakken tsarin kasa baki ɗaya nan da 2030.

Ta kuma ce Shugaban ƙasa Emmanuel Macron zai bayyana matakai da kudaden da za a ware a cikin dabarar yaki da cutar kansa ta kasa na shekarun 2020 zuwa 2030. A cewar National Cancer Institute (INCa), ciwon huhu na ci gaba da zama mafi kisa a Faransa, da sabbin marasa lafiya kusan 52,000 a duk shekara, tare da kusan mutuwar mutane 33,000, inda rahotannin Santé publique France ke nuna cewa mace-macen na raguwa a maza amma na karuwa a mata sakamakon shan taba.

Majiyar Labari: AA