Shugaban Nijar, Janar Abdourahamane Tiani, ya isa Algeria a ranar Lahadi domin wata ziyarar aiki, inda ya gana da Shugaban Algeria Abdelmadjid Tebboune. Ziyarar, wadda ta zo bayan watanni sama da goma na takaddamar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu, ta jawo tarba ta hukuma da karramawa, ciki har da kaɗa taken kasashen da kuma girmamawar rundunar soji.

Tashar talabijin ta ƙasa ta Algeria ta bayyana ziyarar a matsayin wata alama ta zurfin dangantakar tarihi tsakanin kasashen. Manyan jami’an gwamnati da na soja sun halarci tarbar, yayin da shugabannin biyu suka gudanar da tattaunawar sirri tare da wakilan bangarorinsu, kodayake ba a fitar da cikakkun bayanai kan abin da aka tattauna ba.
Masu sharhi na ganin cewa tarbar da aka yi wa Tiani da kuma sabbin matakan diflomasiyya – ciki har da dawowar jakadun kasashen biyu – na nuna karshen barakar da ta samo asali tun bara. Rikicin ya fara ne bayan zargin harbo jirgin mara matuki na Mali, lamarin da ya jawo janye jakadu tsakanin Algeria da kasashen Sahel.

Dangantaka ta fara lafa a ‘yan watannin nan, tare da sake bude tattaunawa kan hadin gwiwar makamashi da manyan ayyukan yankin. Algeria da Nijar na raba iyaka mai tsawon kusan kilomita 950, kuma suna da muhimmiyar hadin gwiwa kan ayyuka kamar Trans-Saharan Highway da shirin bututun gas zuwa Turai.
Majiyar Labari: TRT AFRIKA














