Enas Arbab ta bar Al Fasher a Darfur bayan dakarun RSF sun mamaye birnin, inda ta gudu da ɗanta ƙarami zuwa Masar. Ta ce mahaifinta, Mohamed Arbab, an kashe shi ne bayan an zarge shi da aiki a wurin dafa abinci na sadaka da ke taimaka wa ‘yan gudun hijira. A cewarta, an nemi fansa amma iyalansu sun kasa biya, kuma har yanzu ba su san inda gawarsa take ba.
Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce dubban fararen hula ne aka kashe yayin da RSF ta ƙwace Al Fasher, tare da tilasta wa kusan rabin mazauna birnin tserewa. Rahotanni sun nuna cewa fiye da ma’aikatan wuraren dafa abinci 100 aka kashe tun fara yaƙin, musamman a Darfur da Khartoum, inda rikicin ya fi tsanani.
Ƙungiyoyin agaji sun ce wuraren dafa abinci na al’umma sun zama wata hanyar rayuwa ta ƙarshe ga mutane a yankunan da yunwa da ƙarancin abinci suka addaba. Sai dai ma’aikatan wuraren na fuskantar hare-hare, sacewa da neman fansa, lamarin da ke ƙara tsananta wahalar da fararen hula ke ciki.
Yaƙin Sudan ya ɓarke tun Afrilun 2023 sakamakon rikici tsakanin sojojin ƙasa da rundunar RSF, kuma har yanzu yana ci gaba da haddasa asarar rayuka da tarwatsewar jama’a a sassa da dama na ƙasar.














