Shugaban Nijeriya, Bola Tinubu, ya umarci manyan hafsoshin tsaron ƙasar su nufi Maiduguri domin jagorantar matakan tsaro bayan hare-haren ƙunar-baƙin-wake da suka faru a wurare uku a birnin ranar Litinin. Ya bayyana alhini kan mutuwar mutane tare da jajantawa ga waɗanda suka jikkata da ma al’ummar jihar Borno gaba ɗaya.
A cikin sanarwar da fadar shugaban ƙasa ta fitar, Tinubu ya ce hare-haren wani yunƙuri ne na ƙarshe daga ‘yanta’adda domin tayar da tsoro, yana mai jaddada cewa dakarun tsaro na ci gaba da matsa musu lamba. Ya kuma tabbatar da cewa gwamnati za ta ƙara ƙaimi wajen yaƙar duk wani nau’in ta’addanci a ƙasar.
Hukumomi sun tabbatar da mutuwar aƙalla mutum 23 sakamakon hare-haren, yayin da rundunar Operation Hadin Kai ta gargaɗi yiwuwar sake samun wasu ‘yan ƙunar-baƙin-wake a Maiduguri. Saboda haka, an tura jami’an musamman masu lalata bamabamai domin gano sauran barazanar da ka iya ɓoye.
Tinubu ya yaba wa jarumtakar jami’an tsaro, yana mai cewa Nijeriya ba za ta miƙa wuya ga ta’addanci ba. Ya kuma bayyana cewa an riga an fara ƙara kayan aiki da tallafi ga rundunonin tsaro, tare da umarnin a kula da waɗanda hare-haren ya shafa.














