Nijeriya

‘Yansandan Nijeriya sun kama mutum 48 a samamen da suka kai maɓoyar masu laifi a Zamfara

A cikin wata sanarwa, Kakakin Rundunar ‘Yansandan Jihar, DSP Yazid Abubakar, ya ce aikin da aka gudanar bisa sahihan bayanan sirri ya kai ga nasarar ƙwato babura 17, kekuna uku, janareta guda ɗaya, lasifikoki uku da ganguna uku.

Newstimehub

Newstimehub

4 Aug, 2026

ba0c29bf 82d0 442d ae63 0b84c6d38501 1785828753594

Rundunar ‘Yansandan Jihar Zamfara, tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro, ta kama mutane 48 da ake zargi yayin wani samame da suka kai a maɓoyar masu laifi a cikin birnin Gusau.

A cikin wata sanarwa, Kakakin Rundunar ‘Yansandan Jihar, DSP Yazid Abubakar, ya ce aikin da aka gudanar bisa sahihan bayanan sirri ya kai ga nasarar ƙwato babura 17, kekuna uku, janareta guda ɗaya, lasifikoki uku da ganguna uku, waɗanda ake zargin masu aikata laifuka ne suka bari.

Ya ƙara da cewa ana ci gaba da bincike kan waɗanda aka kama, kuma duk wanda aka samu da laifi za a gurfanar da shi a gaban kotu.

Sanarwar ta ce Kwamishinan ‘Yansandan Jihar Zamfara, Ahmad Muhammad Bello, ya sake jaddada aniyar rundunar ta ci gaba da yaƙi da aikata laifuka da kuma tabbatar da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a faɗin jihar.

Jihar Zamfara na daga cikin jihohin Nijeriya da suka fi fama da hare-haren ‘yanbindiga, inda ƙungiyoyin masu aikata laifuka ke yawan sace mutane domin neman kuɗin fansa, satar dabbobi da kuma kai hare-hare kan al’ummomin karkara.

A watannin baya-bayan nan, jami’an tsaro sun ƙara ƙaimi wajen gudanar da hare-hare domin tarwatsa ƙungiyoyin masu aikata laifuka da kuma dawo da zaman lafiya a jihar.