Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar ya bayyana cewa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ita kaɗai ce jam’iyyar da za ta iya kubutar da Najeriya daga matsalolin tattalin arziki da tsaro da ƙasar ke ciki yanzu. Ya yi wannan furuci ne lokacin ƙaddamar da ofishin ADC na jihar Taraba, bayan ya kammala komawarsa cikin jam’iyyar a hukumance.
Atiku ya ce ya riga ya gwada zama a APC, PDP da sauran jam’iyyu, amma ya fahimci ba su da cikakkiyar hanyar fitar da Najeriya daga halin da take ciki. Ya yi kira ga jama’ar Taraba su yi rijistar zama masu kaɗa kuri’a domin su ceci kansu daga yunwa, talauci, rashin tsaro da rashin aikin yi. Ya kuma nuna cewa wannan yunkuri domin matasa da mata ne, don inganta makomarsu.
Ya kara jan hankalin magoya baya da su rike ADC da gaskiya da amanar jama’a, yana mai ikirarin cewa jam’iyyar za ta lashe Taraba da ma Najeriya baki ɗaya a 2027.














