Afirka

Shugaban Somaliya Ya Gargadi Isra’ila: “Ba Ma Son Ta Kawo Mana Matsalarta”

Shugaban Somaliya Hassan Sheikh Mohamud ya gargadi Isra’ila da kada ta tsoma baki a Somaliland, yana cewa hakan na iya kawo rikice-rikice zuwa yankin Somaliya da gabashin Afirka.

Newstimehub

Newstimehub

1 Jan, 2026

c6c6bd14682160ebe034b9c94c30a1e3fc274a2a165fc0da6d5848e13abea683

Shugaban Somaliya ta nuna tsananin damuwa, domin Hassan Sheikh Mohamud ya bayyana cewa ƙasarsa ba ta son Isra’ila ta kafa ƙafar siyasa ko soji a Somaliland, yana gargadin cewa hakan na iya shigar da rikicin Gabas Ta Tsakiya zuwa yankin Somaliya. A wata hira da TRT World, ya ce Somaliya ba ta taba kawo wa Isra’ila matsala ba, kuma ba ta so a kawo rikice-rikicen Isra’ila zuwa yankinta.

Mohamud ya ce amincewar Isra’ila da yankin da ke neman ballewa daga Somaliya abu ne mai tayar da hankali, yana mai nanata muhimmancin girmama doka da ka’idojin kasa da kasa. Ya yi kira ga duniya da ta goyi bayan matsayin Somaliya, yana mai cewa Mogadishu ta riga ta kai ƙorafi ga Majalisar Dinkin Duniya, Tarayyar Afirka, IGAD, OIC, EAC da ƙungiyar Larabawa, waɗanda suka nuna goyon bayan haɗin kan Somaliya.

Ya bayyana damuwarsa cewa kasancewar Isra’ila a Somaliland na iya ƙara tashin hankali a Tekun Maliya, Gabar Aden da yankin Afirka ta Gabas, yana gargadin yiwuwar yunƙurin kai hari daga ƙungiyoyi kamar Houthi da ƙasashen da ke da sabanin siyasa da Isra’ila. Ya kuma yi watsi da zancen cewa za a iya tsugunar da Falasɗinawa ko kafa sansanin soja a yankin, yana cewa hakan zai jefa Somaliya cikin sabon rikici.

Shugaban ya kuma gode wa Turkiyya kan rawar da take takawa wajen sasanci da tallafi ga Somaliya, yana mai cewa akwai ƙarfafa haɗin gwiwa a bangaren tsaro, diflomasiyya da tattalin arziki. Ya ce Somaliya za ta ci gaba da neman mafita cikin lumana ga batun yankin arewa, ba tare da tilas ba.

Majiyar Labari: TRT HAUSA