Nijeriya

Fashewar Bam a Zamfara Ta Hallaka Mutane a Hanyar Magami–Dansadau

Fashewar bam da aka binne a hanya a Zamfara ta yi sanadin mutuwar aƙalla mutane bakwai tare da jikkata wasu da dama.

Newstimehub

Newstimehub

28 Dec, 2025

dauda e1767031163281

Aƙalla mutane bakwai ne suka rasa rayukansu yayin da wani bam da aka binne a kan hanya ya tashi a titin Magami zuwa Dansadau, a Jihar Zamfara, ranar Asabar. Rundunar ‘yansandan jihar ta tabbatar da faruwar lamarin, wanda ya auku da misalin ƙarfe 2:30 na rana a ƙauyen Maikogo, ƙaramar hukumar Maru.

A cewar kakakin rundunar ‘yansandan jihar, DSP Yazid Abubakar, bam ɗin ya tarwatsa wata tirela gaba ɗaya, inda ba a iya gane motar, kuma ya yi sanadin mutuwar mutane da dama, ciki har da wani mai babur da ya tsinci kansa a wurin a lokacin fashewar.

Ko da yake rundunar ba ta bayyana takamaiman adadin waɗanda suka mutu ko suka jikkata ba, rahotannin kafofin watsa labarai sun nuna cewa aƙalla mutane bakwai ne suka mutu. Rundunar ‘yansanda ta ce ta riga ta fara bincike domin gano waɗanda ke da hannu a lamarin.

A nasa bangaren, kakakin gwamnan Zamfara, Mustapha Kaura, ya bayyana cewa ‘yan bindiga ne ake zargi da dasa bam ɗin, musamman a lokacin da suke tserewa bayan da jami’an tsaro suka kai musu hari, ciki har da kisan wani shahararren jagoransu.

Majiyar Labari: Trt Hausa