Bankunan Najeriya na ƙara zage dantse domin cika sabon sharadin ƙarin jarin da Babban Bankin Najeriya (CBN) ya kafa, yayin da ake shirin kammala aikin sake ƙarfafa bankuna kafin wa’adin 31 ga Maris 2026.
Da saura kwanaki 52 kacal na aiki, hukumomi da masana harkokin kuɗi sun ce yawancin bankuna sun fara neman jari ta hanyoyi daban-daban, ciki har da jawo hannun jarin masu kuɗi da rage matakin lasisin banki daga na ƙasa zuwa na yanki ko daga na duniya zuwa na ƙasa. CBN ta tabbatar da cewa fiye da bankuna 20 sun riga sun cika sharuddan, yayin da wasu ke ci gaba da ƙoƙarin tara kuɗin da ake buƙata a ƙarƙashin sabon tsarin da ke la’akari da jarin hannun jari kaɗai.
Majiyar Labari: TVC NEWS














