Ministan Harkokin Wajen Türkiye, Hakan Fidan, ya bayyana cewa lokaci ya yi da za a tabbatar da haɗin kan ƙasa a Syria, yana mai kira ga Syrian Democratic Forces (FDS) da su ɗauki nauyin da ya rataya a wuyansu maimakon zama kayan aiki ga manufofin Isra’ila. Ya yi wannan jawabi ne a wani taron manema labarai tare da Ministan Harkokin Wajen Oman, Bedr bin Hamed al-Busaidi.
Fidan ya ce juyawar da FDS ke yi zuwa abin amfani wajen aiwatar da manufar Isra’ila ta “raba mutane domin mulki” ba abin da ya zo kwatsam ba. Ya bayyana cewa hakan na ci gaba da barazana ga zaman lafiyar Syria a daidai lokacin da ake bukatar dunkulewar ‘yan ƙasa da haɗin kai tsakanin bangarori.
Ministan ya danganta tashin hankalin da aka gani a Aleppo da gargadin da Ankara ta rika yi tun kusan shekara guda, yana mai cewa da a ce PKK/YPG — wanda Türkiye ke kallon sa a matsayin ƙungiyar ta’addanci da ke aiki da sunan FDS — ya shiga tsarin haɗewa da gwamnatin Syria da wuri, da ba a kai ga wannan rikici ba. Ya ƙara da cewa riƙe yankuna da ƙarfi ba tare da sassauci ba ba ya amfani ga kowa.
A ƙarshe, Fidan ya bayyana cewa Türkiye na kallon abubuwan da ke faruwa a Yemen, Somaliland, Sudan da Syria ta fuskar tsari ɗaya na dabarun tsaro, yana mai jaddada cewa Ankara za ta ci gaba da bin waɗannan batutuwa a matsayin lamurra masu alaƙa da juna a yankin.














