Siyasa

Ghana Ta Kira Jakadanta daga Nijeriya Kan Zargin Maguɗin Zaɓe

Gwamnatin Ghana ta kira jakadanta daga Nijeriya nan take bayan zargin hannunsa a maguɗin zaɓe a Ayawaso East, domin kare gaskiya da ɗa’ar aiki.

Newstimehub

Newstimehub

9 Feb, 2026

10a78afc ba58 491e 9b19 6e65f61ec637

Ghana ta yi wa jakadanta a Nijeriya, Baba Ahmed, kiranye nan take biyo bayan zargin hannu a maguɗin zaɓe a zaɓen fid da gwani na ‘yan majalisu a mazaɓar Ayawaso East. Matakin ya zo ne bayan rahotannin da ke zargin Ahmed—wanda shi ma mai neman takara ne—da taka rawa a maguɗin zaɓe a matsayinsa na jami’in gwamnati.

Wata sanarwa daga fadar shugaban ƙasa a Accra ta ce kiranyen ya fara aiki nan take, domin kauce wa duk wani tunani na rashin adalci ko karya dokokin ɗa’ar aiki ga masu rike da mukaman siyasa. Sanarwar ta jaddada cewa ci gaba da zamansa a ofis ba zai dace ba a irin wannan yanayi.

cefb9de794dbaa01bda003bd3a56af64e194070b23658fad5e48f7638826251f

Shugaban Ghana, John Mahama, ya bayyana cewa matakin wani bangare ne na kare sahihancin tsarin dimokuraɗiyya da tabbatar da gaskiya a harkokin siyasa. A lokaci guda, an kuma zargi wasu ‘yan takara a zaɓen fid da gwani da laifin sayen ƙuri’u—zargin da ke kara tayar da hankalin jama’a kan sahihancin zaɓen.

Majiyar Labari: TRT HAUSA