Jam’iyyar APC mai mulki a Nijeriya ta yi nasara a zaɓukan cike gurbi na Majalisar Dokokin Jihar Kano da aka gudanar a ranar Asabar. An shirya zaɓukan ne domin cike guraben da suka kasance babu kowa bayan rasuwar ‘yan majalisa biyu a watan Disambar bara.
‘Ya’yan mamatan, Aminu Sa’adu Jr. da Nabil Daneji, sun tsaya takara a ƙarƙashin APC. A Kano Municipal, Daneji ya samu ƙuri’u 7,484, inda jami’in tattara sakamako Ibrahim Siraj ya ayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara.
A mazabar Ungogo kuma, ɗan takarar APC Sa’ad ya lashe kujerar da ƙuri’u 8,975, kamar yadda jami’in tattara sakamako Ali Abdullahi ya sanar. Hukumar INEC ta ce zaɓukan sun gudana cikin kwanciyar hankali.
Kwamishinan zaɓe na Kano, Abdu Zango, ya danganta ƙarancin fitowar masu kaɗa ƙuri’a da lokacin da aka gudanar da zaɓen da kuma ƙarancin shiga daga jam’iyyun siyasa.
Majiyar Labari: TRT HAUSA














