Nijeriya Tsaro

Sojojin Nijeriya Sun Kuɓutar da Fasinjoji 18 daga ‘Yanfashin Teku a Gaɓar Kamaru

Dakarun Birged ta 13 sun kuɓutar da fasinjoji 18, ciki har da yara biyu, bayan ‘yanbindiga sun yi garkuwa da su a teku yayin tafiya zuwa Kamaru.

Newstimehub

Newstimehub

12 Jan, 2026

b1103e2acb18e563c0bc8b46402cf972866dc12f81b3d995721c51a388f13fc1

Sojojin Nijeriya sun samu nasarar ceto mutum 18, ciki har da ƙananan yara biyu, daga hannun ‘yanfashin teku da suka yi garkuwa da su a yayin da suke tafiya a kwalekwale daga Nijeriya zuwa Kamaru. Rundunar ta ce lamarin ya faru ne a gaɓar tekun Kombo Fishing Port da ke yankin Kamaru.

A cewar mataimakin mai magana da yawun Birged ta 13, Manjo Yemi Sokoya, dakarun da ke Ikang sun bi sawun ‘yanfashin tekun bayan sace fasinjojin, inda aka yi musayar wuta har sai da ɗaya daga cikin kwalekwalensu ya kife. Daga bisani ‘yanfashin suka tsere zuwa daji, suka bar dukkan mutanen da suka yi garkuwa da su, waɗanda aka ceto su lafiya ba tare da wani rauni ba.

Majiyar Labari: TRT HAUSA