Shugaban Ghana, John Mahama, ya tashi daga Accra ranar Lahadi zuwa Birtaniya, inda zai gana da masu tsara shirin Accra Reset Initiative, kafin ya wuce Davos, Switzerland, domin halartar wani zama na World Economic Forum (WEF).
A cikin wata sanarwa da Felix Kwakye Ofosu, kakakin fadar shugaban ƙasa kuma Ministan Jiha mai kula da harkokin sadarwar gwamnati, ya fitar, an ce Mahama zai kuma yi taron ganawa na ƙashin kai (bilateral meetings) da wasu shugabannin duniya a gefen taron Davos.














