Hukumar NAFDAC ta kulle rumbuna 18 a wasu sassan Jihar Niger bayan da ta gano tarin kayayyakin abinci da suka wuce wa’adin amfani, wadanda kudinsu ya kai sama da Naira miliyan 100.
Rahotanni sun ce an gano wasu daga cikin kayayyakin an taba su kafin a mayar da su kasuwa, lamarin da hukumar ta bayyana a matsayin babbar barazana ga lafiyar al’umma.
Hukumar ta tabbatar da cewa an rufe dukkan rumbunan da abin ya shafa, yayin da ake ci gaba da bincike domin gano wadanda ke da hannu a lamarin tare da gurfanar da su a gaban kuliya.

NAFDAC ta kuma gargadi masu hannu a irin wannan haramtacciyar sana’a cewa za su fuskanci hukunci mai tsauri bisa dokokin kasa. Ta bukaci masu saye su rika duba ranar karewar kaya kafin saya, tare da kai rahoton duk wani abu da ake zargi ga hukumomi.
Majiyar Labari: TVC NEWS














