Gwamnatin Jihar Jigawa tare da tallafin WHO ta lalata katunan noodles 5,520 da suka kare wa lokaci a Dutse, domin kare lafiyar al’umma da kuma tabbatar da amincewar jama’a ga shirye-shiryen rigakafi a ƙasar. An gudanar da aikin gaban jami’an WHO, ’yan sanda, NSCDC, hukumar kare muhalli ta jihar (JISEPA), da kafafen yaɗa labarai.
Noodles ɗin an kawo su ne a matsayin kayan ƙarfafa halarta a lokacin shirin rigakafin National Immunisation Plus Days, amma saboda dagewar shirin daga Nuwamba zuwa 2 Disamba 2025, kayayyakin suka kai ranar “best before” dinsu. Daga nan gwamnati ta tattara su daga kananan hukumomi 27 na jihar, ta lalata su ta hanyar kona su domin kada su shiga hannun jama’a.
Jami’in sarkar sanyi na jihar, Yusuf Inuwa, ya ce barin irin waɗannan kayayyaki su shiga hannun mutane na iya jawo matsalolin lafiya, ciki har da guba daga abinci. Gwamnatin Jigawa ta ce wannan matakin na nuna jajircewarta wajen kare lafiyar jama’a da tabbatar da amincewa da shirye-shiryen rigakafi a Najeriya.














