Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya ƙaddamar da Tsarin Tattalin Arzikin Halal na Ƙasa domin bai wa ƙasar damar cin gajiyar kasuwar halal ta duniya wadda darajarta ta kai dala tiriliyan 7.7.
Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima, wanda ya wakilce shi a Abuja, ya ce ana sa ran shirin zai ƙara dala biliyan 1.5 ga tattalin arzikin ƙasa nan da 2027, tare da bunƙasa fitar da abinci halal, magunguna, kayan kwalliya, yawon buɗe ido, da hanyoyin kuɗi masu ɗa’a.
Gwamnati ta ce shirin zai samar da darajar tattalin arziki da ta haura dala biliyan 12 nan da 2030 tare da ƙarfafa ƙananan da matsakaitan ‘yan kasuwa.
Majiyar Labari: TRT HAUSA














