Shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro, ya ba da umarnin ɗaukar ƙarin dubban jami’an tsaro

Shugaba na Nijeriya Tinubu ya kuma buƙaci majalisar dokokin kasar ta sake duba dokokin da za su bai wa jihohi damar kafa ‘yan sanda, ya kuma yi kira ga cibiyoyin addini da su nemi kariya a lokacin taruka.
27 Nov, 2025
An sako ‘yan matan makarantar sakandaren Jihar Kebbi 24 da ‘yan bindiga suka sace

Bayanai na cewa an kuɓutar da ‘yan matan ne da safiyar Talata ta hanyar tattaunawa, kuma tuni suka ƙarasa birnin Kebbi, babban birnin jihar a cikin daren Talata, kamar yadda Kwamishinan Labarai Jihar Yakubu Ahmed BK ya shaida wa TRT Afirka.
25 Nov, 2025
Majalisar Wakilan Nijeriya ta ce ana samun ƙaruwar zamba ta POS da ayyukan kirifto ba bisa ƙa’ida ba

Olufemi Bamisile, Shugaban kwamitin, wanda ke jawabi a wani zaman bincike ya ce ayyukan masu ruwa da tsaki sun nuna manyan giɓi a fannin harkokin kudi na dijital na Nijeriya.
25 Nov, 2025
‘Yan bindiga sun sace mutum takwas a karamar hukumar Tsanyawa a Jihar Kano

Dan majalisar tarayya mai wakiltar yankin, Injiniya Sani Bala Tsanyawa ya tabbatar wa TRT Afrika da labarin, sai dai ya ce zuwa yanzu ba su kammala tattara alƙaluman yawan mutanen da aka ɗauke ba.
25 Nov, 2025

Gwamnonin Kudu maso Yammacin Nijeriya sun sabunta kira kan samar da ‘yan sandan jihohi

Nijeriya na fuskantar yunwa mafi muni a tarihi saboda hare-haren ‘yan bindiga da rage tallafi: MDD

Amurka za ta tallafa wa Nijeriya da bayanan sirri da kayayyakin tsaro – Fadar Shugaban Nijeriya

Tinubu ya yi ganawar sirri da manyan jami’an tsaron Nijeriya

Ɗalibai 50 cikin fiye da 300 da aka sace daga makarantar St. Mary a Jihar Neja sun tsere – CAN
23 Nov, 2025
Gwamnatin Kebbi ta bayar da umarnin rufe duka makarantun gwamnati da na kuɗi a jihar
Wannan na zuwa ne bayan sace ɗalibai mata 25 daga wata makaranta da ke Maga.

21 Nov, 2025
Hukumar NDLEA ta kama mutum 230 a samame daban-daban a Kano
An kai samamen ne a maɓoyar fitattun masu safarar ƙwayoyi a yankuna kamar su Kofar Ruwa, Tashar Rami, Rijiyar Lemo, Kurna, Mil Tara da sauran wurare da dama inda aka ƙwato tabar wiwi da sholisho da miyagun ƙwayoyi da makamai.

21 Nov, 2025
Jerin lokutan da aka shafe ana shari’ar Nnamdi Kanu, jagoran ‘yan-awaren Biafara a Nijeriya
An fara kama shi ne a shekarar 2015 bisa zarginsa da laifin cin amanar kasa da kuma zama mamba na kungiyar da ba ta kan ka’ida.

21 Nov, 2025
‘Yan bindiga sun sace ɗalibai da ma’aikata a wata makaranta a Jihar Neja
Bayanai na cewa, maharan sun afka makarantar ne da misalin karfe biyu zuwa uku na dare, inda suka tafi da dalibai da ma’aikatan, sai dai har kawo yanzu babu bayani kan adadin mutanen da harin ya shafa.

20 Nov, 2025
Jagoran ‘yan-awaren Biafra: Babbar Kotu a Nijeriya ta samu Nnamdi Kanu da laifin ta’addanci
Alƙalin kotun ya ce masu shigar da ƙara sun kawo shaidun da suka nuna cewa Nnamdu Kanu ya tunzura munanan hare-haren kan jami’an tsaro da kuma ‘yan Nijeriya da ke kudu maso gabashin Nijeriya.

20 Nov, 2025
Ribadu ya jagoranci wata tawagar Nijeriya mai ƙarfi zuwa Amurka kan zargin kashe Kiristoci a ƙasar
Tun bayan zargin da Amurka ta yi kan kashe Kiristoci a Nijeriya, gwamnatin ƙasar ta musanta wannan zargin amma duk da haka Amurka ta ci gaba da tafiya a kan ra’ayinta kan cewa ana zaluntar Kiristoci a Nijeriya.

20 Nov, 2025
Kotu ta yanke wa wani shugaban ISWAP da ya tsara hare-haren kano na 2012 ɗaurin shekara 20
Mai shari’a Emeka Nwite ne ya yanke hukuncin a ranar Laraba bayan samun Ismaila da aka fi sani da Mai Tangaran da laifukan shirya hare-haren ta’addanci a Kano ranar 20 ga Janairun 2021, wadanda suka yi sanadiyyar mutuwar mutane sama da 150.

19 Nov, 2025
Majalisar Dattawan Nijeriya ta nemi a ɗauki ƙarin sojoji 100,000 don magance rashin tsaro
Gidan talabijin ɗin ƙasar (NTA) ya ruwaito cewa majalisar ta kuma kafa wani kwamiti na wucen gadi domin yin bincike kan ware kuɗi da kashe kuɗi da kuma sakamakon shirin kare makarantu.

19 Nov, 2025
Tinubu ya ɗaga tafiyarsa tarukan G20 da AU-EU saboda yanayin rashin tsaro da ake ciki a Nijeriya
Tun da fari an tsara cewa Shugaba Tinubu zai bar Abuja a ranar Laraba don halartar Taron G20 karo na 20 a Afirka ta Kudu, inda daga can zai wuce Luanda don halartar taron Ƙungiyar Hadin Kan Afirka da na Tarayyar Turai wato AU-EU.

19 Nov, 2025
Tinubu ya yi alhinin mutuwar Janar Uba da ‘yan ta’adda suka kashe a Borno
Shugaban na Nijeriya ya kuma yi magana game da ɗalibai 25 da aka sace a makarantar ‘yan mata ta gwamnati a ƙaramar hukumar Danko/Wasagu ta jihar Kebbi ranar Litinin.



