Ajanda Wasanni

Premier League Za Ta Dakatar da Wasanni na Ɗan Lokaci Domin Iftar a Ramadan

Premier League za ta ba da damar dakatar da wasa na ɗan lokaci a Ramadan domin ‘yan wasa Musulmai su karya azumi.

Newstimehub

Newstimehub

17 Feb, 2026

download

Rahotanni daga kafafen yada labarai na Birtaniya sun ce Premier League za ta ba da damar dakatar da wasa na ƴan mintuna a lokacin faduwar rana a watan Ramadan, domin ‘yan wasa Musulmai su karya azumi. An ce alkalai za su duba kafin fara wasa ko akwai ‘yan wasan da ke azumi.

Idan aka tabbatar akwai masu azumi, wasa na iya tsayawa a lokacin iftar, inda ‘yan wasa za su samu damar shan ruwa ko karin kuzari kafin a ci gaba da wasa. Wannan mataki na nufin tallafa wa ‘yan wasa ba tare da kawo cikas ga wasan ba.

An fara lura da irin wannan tsari a watan Afrilu 2021, lokacin wasan Leicester City da Crystal Palace. A wancan lokaci, an dakatar da wasa na ɗan lokaci domin Wesley Fofana da Cheikhou Kouyaté su karya azumi, kafin a koma ci gaba da wasa.

Tun daga lokacin, irin wannan dakatarwa ta Ramadan ta zama ruwan dare a kwallon kafa ta Ingila, inda aka karɓe ta da kyau a matsayin mataki mai amfani da ke mutunta ibadar ‘yan wasa.

Majiyar Labari: TRT WORLD