Shugaban Jamhuriyar Kongo, Denis Sassou Nguesso, ya sanar a ranar Alhamis cewa zai sake neman wa’adi a zaɓen shugaban ƙasa da za a gudanar a Maris, yana mai fatan ci gaba da mulkinsa duk da shekarunsa 82. Ya bayyana hakan ne a gaban dubban magoya baya a yankin Ignie da ke kudancin ƙasar.
Dokar ƙasar ba ta hana Nguesso tsayawa takara ba, bayan gyaran kundin tsarin mulki na 2015 da ya cire iyakar shekaru 70 tare da kafa wa’adi uku na shekaru biyar-biyar. Nguesso ya mulki Kongo-Brazzaville tun daga 1979 zuwa 1992 a tsarin jam’iyya ɗaya, kafin a kayar da shi a zaɓen dimokiraɗiyya na farko. Sai dai ya dawo kan karagar mulki a 1997 bayan yaƙin basasa, kuma tun daga lokacin yake mulki.
Jam’iyyar sa mai mulki, Congolese Labour Party (PCT), ta riga ta sanar a watan Disamba cewa shugaban zai nemi sabon wa’adi. A zaɓen 2021, Nguesso ya lashe kujerar shugaban ƙasa da sama da kashi 88% na ƙuri’u.
Majiyar Labari: TRT AFRIKA














